• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudurinsa Na Bai Wa Ɓangaren Shari’a ‘Yanci Don Samar Da Adalci A Zamfara

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudurinsa Na Bai Wa Ɓangaren Shari’a ‘Yanci Don Samar Da Adalci A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta duƙufa wajen ba da fifiko ga tsare-tsare da ke inganta tabbatar da adalci a kan lokaci da kuma kare ’yancin ɓangaren shari’a.

 

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Litinin ɗin da ta gabata a wajen taron ƙara wa juna sani ga alƙalai da ma’aikatan kotuna a babbar kotun shari’a ta Jihar Zamfara, wanda aka gudanar a harabar babbar kotun da ke Gusau.

  • Babbar Kasa Mai Farar Aniya: Shin Har Yanzu Akwai Masu Son Lalata Dangantakar Sin Da Afrika?
  • Nakasa A Mahangar Karin Magana: Guzurin Ranar Nakasassu Ta Duniya

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, taron ya samar da wata dama ga jami’an shari’a da masu ruwa da tsaki domin tantance ayyukan da bangaren shari’a ke yi, da gano ƙalubale, da kuma kafa sabbin manufofi.

 

Labarai Masu Nasaba

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

A jawabinsa na bufe taron, Gwamna Lawal ya amince da jajircewa da jagoranci na ƙwarai na Babbar Alƙalin Alƙalan Jihar, Mai Shari’a Kulu Aliyu, OFR, FNJI, da ɗaukacin bangaren shari’a bisa jajircewarsu na sauke nauyin da aka ɗora musu.

 

Ya ce, “jajircewarta wajen tabbatar da adalci yana ƙara ƙwarin gwiwa da kuma ƙara wa bangaren shari’a aminci a matsayin wata cibiya mai muhimmanci a tsarin dimokuraɗiyya. Wannan gwamnati ta tsayu tsayin daka wajen tallafa wa bangaren shari’a a dukkan ayyukanta.

 

“Gwamnatina za ta ci gaba da ba da fifiko ga shirye-shiryen da za su inganta samar da adalci a kan lokaci da kuma kare ‘yancin wannan bangare na gwamnati.”

 

Gwamna Lawal ya bayyana cewa, taron ƙara wa juna sanin na da matuƙar muhimmanci. “Zai inganta fasaha da kuma ilimantar da mahalarta domin su kasance cikin shiri sosai don yin hidima da biyan buƙatun jama’a. Jama’ar mu na kallon ku a matsayin matita ga talakan ƙasa wajen ganin ya samu adalci tare da kare haƙƙinsa. Dole ne jami’an shari’a da ma’aikatan su kasance cikin shiri sosai don cimma waɗannan manufofi, musamman a waɗannan lokutan da ake fuskantar ƙalubale.

 

“Babbar Alƙalin Alƙalai, alƙalan babbar kotun jihar Zamfara, manyan mahalarta taron, abin farin ciki ne ganin irin matakan da hukumar shari’a ke ɗauka wajen tsare-tsaren ma’aikatan Majistare da sauran ma’aikatan shari’q domin tabbatar da adalci.

 

Gwamnan ya kuma buƙaci bangaren shari’a da su yi taka-tsan-tsan a kan wasu ’yan tsirarun da ɗabi’unsu za su iya gurgunta mutuncin wannan hukuma. “Ganowa tare da magance rashin ɗa’a a bangaren wani nauyi ne da ke buƙatar himma, mutunci, da sadaukarwa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rabiu Ali Ya Samu Gayyata Domin Wakiltar Nijeriya A Wasannin CHAN

Next Post

Sin Ta Yi Maraba Da Amincewar Da UNGA Ya Yi Da Kudurin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Kasar Ta Gabatar

Related

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya
Labarai

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

5 hours ago
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano
Labarai

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

5 hours ago
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari
Labarai

Za A Dinga Tunawa Da Buhari A Matsayin Waliyyi A Siyasar Nijeriya —Dakta Zangina

6 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

7 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Shirin Yi Wa Dangote Zanga-zanga Kan Rage Farashin Gas

7 hours ago
Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba
Ra'ayi Riga

Lai Ching-Te Bai Cancanci Zama Jagoran Yankin Taiwan Ba

8 hours ago
Next Post
Sin Ta Yi Maraba Da Amincewar Da UNGA Ya Yi Da Kudurin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Kasar Ta Gabatar

Sin Ta Yi Maraba Da Amincewar Da UNGA Ya Yi Da Kudurin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Kasar Ta Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.