ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
majalisar kasa

Neman kirkirar sabbin jihohi da kananan hukumomi da ‘yansanda jihohi da saka sarakuna cikin sha’anin harkokin mulki da sauran su, su suka dabaibaye sauraron jin ra’ayoyin jama’a kan gyaran kundin tsarin mulki na jihohin arewa a wannan karshen mako.

Kwamitin Majalisar Wakilai na duba gyaran tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya gudanar da taron jin ra’ayoyin jama’a a karshen mako a yankuna na arewa maso yammacin Nijeriya da arewa ta tsakiya da arewa maso gabas don samun shawarwari daga masu ruwa da tsaki daban-daban domin ba wa ‘yan majalisar damar yin gyare-gyare a kundin tsarin mulki na shekarar 1999.

Kwamitin ya bayyana cewa ya karbi bukatu 46 na neman kirkirar sabbin jihohi, tare da bukatu 117 na kirkirar sabbin kananan hukumomi a fadin kasar nan, yana mai cewa an samu shawarwarin ne daga kungiyoyi daban-daban da ke dukkan fadin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Rahotoni sun bayyana cewa an yi yunkurin gyaran kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999, wanda wasu lauyoyi da masu nazari suka bayyana a matsayin dabtarin da bai dace da ka’idojin dimokuradiyya ba, bayan shekaru da dama na mulkin soja.

Yunkurin ya haifar da karin kashe kudade, amma kuma ya haifar da sakamako mai kyau a baya, wanda aka kiyasta cewa, gyaran kundin tsarin mulki ya lakumi naira biliyan 20 tare da sauye-sauyen abubuwa 30 da aka yi wa kundin a cikin shekaru 20 da suka wuce.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Jagoran majalisar dattawa, Opeyemi Bamidele, ya bayyana cewa majalisa za ta gabatar da rahoton sake duba kundin tsarin mulki wanda ake yi a halin yanzu ga majalisun jihohi 36 kafin watan Disamba na shekarar 2025.

 

Arewa Ta Gabas

A zaman jin ra’ayi na yanki a arewa ta Gabas, wanda aka gudanar a jihohin Borno da Gombe, kwamitin ya karbi shawarwari guda bakwai don kirkirar sabbin jihohi da kuma kirkirar kananan hukumomi fiye da 40 daga kungiyoyi daban-daban.

Masu ruwa da tsaki sun kira ga samar da Jihar Amana daga Adamawa, Jihar Sabannah daga Borno, Jihar Katagum daga Bauchi, Jihar Tangalwaja daga Gombe da Muri, Jihar Kwararafa da Jihar Sardauna ta Kudu daga Taraba.

Wani muhimmin bukatu da kungiyoyin suka gabatar sun hada da kujeru na musamman ga mata, rarraba iko da kuma gudummuwar sarakuna a tsarin mulkin Nijeriya.

Shugaban taron na yankin arewa maso gabas ‘B’, Hon Isa Ali wanda ya kunshi jihohin Borno, Yobe da Adamawa, ya ce ya karbi shawarwari daga sama da kungiyoyi 50.

Haka nan, a arewa maso gabas ‘A’, a Gombe, wanda shugabanta shi ne mai tsawatarwa na majalisa, Rt.Hon. Usman Bello Kumo, ya bayyana cewa an karbi fiye da gungun shawarwari 30 daga kungiyoyi daban-daban, kungiyoyin addini da na gargajiya, da kuma mutane masu neman canje-canje ko gyare-gyare a kundin tsarin mulki.

 

 Arewa Ta Tsakiya

A arewa ta tsakiya kuwa, fafutuka na neman kirkirar karin jihohi da hukunta gwamnonin jihohi da suka gaza ba da ‘yancin kai ga kananan hukumomi da kirkirar karin yankunan kananan hukumomi da kuma ‘yansandan jihohi sun mamaye sauraron jin ra’ayoyi jama’a.

Sauran su ne ikon jihohi na tsara dokoki da kula da bangaren hakar ma’adanai da kuma bai wa mata karin karo mai tsoka cikin harkokin gwamnati.

An gabatar da bukatun daga masu ruwa da tsaki a taron bainar jama’a na yankin ‘A’ da aka gudanar a cibiyar taro na Siyyam da ke Minna a Jihar Neja. Cibiyar ‘A’ ta kunshi jihohin Neja, Kwara da Kogi.

An ba da shawarar kirkiran jihohi da suka hada da Kainji da Edu daga Neja da Kebbi da Okura da Okun daga Jihar Kogi da Ifesuwakpo daga Jihar Kwara.

Shugaban kwamitin jagororin taron don kafa Jihar Kainji, Amb. Ahmed Musa Ibeto, tsohon mataimakin gwamnan Jihar Neja, ya ce Jihar Kainji wadda ya kamata ta kunshi masarautun Borgu da Kontagora a Jihar Neja da Masarautar Zuru a Jihar Kebbi, za ta rage wuraren da ba a gudanar da su ba da yanzu haka masu fashi ke mamaye, kuma za ta taimaka wajen yaki da ta’addanci.

 

Arewa Maso Yamma

A lokacin taron jin ra’ayoyin jama’a na yankin arewa maso yamma yankin ‘A’ na majalisar wakilai da aka gudanar a Kaduna, masu ruwa da tsaki sun nemi a kirkiro sabbin jihohi da ‘yansandan jihohi da kuma ware kujeru na musamman ga mata a majalisa.

Wakilan daga jihohin Kano, Katsina, Jigawa, da Kaduna sun gabatar da takardun ra’ayi kan gyaran tsarin mulki, musamman ma kan rarraba iko da gwanati ga kowani bangare na kasar nan.

Taron, wanda mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai, Hon. Madaki Aliyu, ya jagoranci kwamitin wanda ya jawo hankulan masu ruwa da tsaki, ciki har da kungiyoyin matasa, kungiyoyin kwadago, kungiyoyin addini, masana shari’a da kungiyoyin mata.

Tsarin Mulki
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa
Tsarin Mulki
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
  • Sulaiman
    Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.