• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Majalisar Zartaswa Kan Tattara Kudin Fansho

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Jagoranci Taron Majalisar Zartaswa Kan Tattara Kudin Fansho
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Litinin ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman majalisar zartarwa ta jihar Zamfara.

A wajen taron, Gwamna Dauda Lawal ya karbi bayani daga kwamitin da aka kafa domin tabbatar da matsayin kudaden fansho na jihar Zamfara da na kananan hukumomi.

  • Rikicin Ribas: Tinubu Ya Shiga Tsakanin Fubara Da Wike
  • Babu Shirin Sake Sauya Fasalin Naira — CBN

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce taron da aka gudanar a zauren majalisar da ke gidan gwamnati da ke Gusau, an tattauna batutuwan da suka shafi ci gaban jihar Zamfara.

Ya kara da cewa majalisar ta samu rahoton ci gaban da aka samu na shirin ingantawa da zamanantar da filin wasa na tunawa da Sardauna Gusau da dai sauransu.

Ya ce: “A ranar 9 ga Oktoba, 2023, Majalisar zartaswa ta Jihar Zamfara ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin Shugaban Ma’aikata, domin tantance matsayin da Jihar Zamfara ta ke da shi na bayar da gudunmawar fansho na kananan hukumomi.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

“Yayin da yake yi wa majalisar bayani, Shugaban kwamitin kuma shugaban ma’aikata na jihar Zamfara Ahmad Aliyu Liman ya bayyana cewa manufar kwamitin ita ce ta binciki zargin karkatar da kudaden da aka zaftare daga albashin ma’aikatan jiha da na kananan hukumomin jihar kan shirinsu na fansho.

“Wadannan kudade ya kamata a mika su ga masu kula da asusun fansho (PFAs) wadanda ke da alhakin kula da asusun ajiyar ma’aikata (RSAs) a jihar.

“Shugaban kwamatin ya bayyana cewa rashin fitar da kudaden ya saba wa dokar fansho ta (2014) da ke tafiyar da tsarin tafiyar da kudaden fansho kamar yadda hukumar fansho ta kasa (PenCom) ta tsara.

“Ya kuma kara nanata cewa rashin kudin da aka samu ya haifar da gazawar Hukumar Kula da Kudaden Fansho (PFAs) ta kasa biyan kudin fansho da na wadanda suka mutu yadda ya dace, wanda hakan ya haifar da koma baya ga kudaden da ba a biya ba a halin yanzu ya yi wa Gwamnatin Jiha yawa.

“Gwamna Lawal a matsayinsa na Shugaban Majalisar Zartaswa, ya bayyana aniyar bayar da tallafin da ya dace don kai dauki ga duk wani abu da ba a biya ba,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FanshoZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Ribas: Tinubu Ya Shiga Tsakanin Fubara Da Wike

Next Post

CBN Ya Rufe Wasu Bankuna 754 Sakamakon Shiga Matsaloli

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

2 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

4 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

5 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

9 hours ago
Next Post
CBN Ya Rufe Wasu Bankuna 754 Sakamakon Shiga Matsaloli

CBN Ya Rufe Wasu Bankuna 754 Sakamakon Shiga Matsaloli

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.