• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 546 Na Shekarar 2025

by Sulaiman and Hussein Yero
6 months ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 546 Na Shekarar 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗin shekarar 2025 na Naira 546,014,575,000.00.

 

Kasafin kuɗin 2025 mai taken; “Kasafin Ceto 2.0”, kakakin majalisar dokokin jihar Zamfara ya gabatar wa gwamnan a ranar Alhamis a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau.

  • Dakarun MNJTF Sun Daƙile Harin Da Aka Kai Sansanin Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10 A Kamaru
  • Dubun Sojan Gona Ta Cika Bayan Damfarar Mutane A Jihar Yobe

A yayin rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2025, Gwamna Lawal ya ƙuduri aniyar kammala dukkan ayyukan da ake gudanarwa tare da inganta nasarorin da aka samu a cikin watanni 18 da gwamnatinsa ta yi.

 

Labarai Masu Nasaba

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

Gwamnan ya bayyana muhimmancin kasafin kuɗin shekarar 2025, inda ya ce ‘ba wai kawai mu kalli inda muke ko kuma inda muka dosa ba, amma inda muka kasance’.

 

“Abin ya tsananta a bara. Shekaru goma na rashin shugabanci nagari ya haifar da durƙushewar tattalin arziki, rashin biyan ma’aikatan gwamnati albashi, da kuma basussukan da ke kawo cikas ga ilimin yara. An lalata ababen more rayuwa, an yi watsi da asibitoci, kuma ayyukan jama’a sun ɗaiɗaita. Bugu da qari kuma, akwai rashin bin doka da oda, da batun kuɗin wutar lantarki da ake ci gaba da yi, da rashin isasshen ruwan sha, rashin tsaro, da ƙaruwar cututtuka masu yaɗuwa kamar kwalara, tare da raguwar kuɗaɗen shiga na cikin gida.

 

“Da ba mu yi gaggawar magance dukkan ƙalubalen ba, da jihar Zamfara ba za ta zama wurin da dukkan mu za mu iya rayuwa a yau ba.

 

“Ƙudirin Ceto na 2025 2.0 yana gudana ne ta hanyar jajircewarmu na ci gaba da ayyukan da muka fara wa mutanenmu, wanda ke nuna kyawawan manufofi na kishi. Wannan kasafin kuɗin kuma ya sanya aka ƙara wa ma’aikata ƙarin albashi mafi ƙaranci, inda ya tashi daga N30,000 zuwa N70,000.

 

Gwamna Lawal ya bayyana cewa lokaci ya yi da jihar Zamfara za ta shawo kan lalacewar ababen more rayuwa da kuma ƙoƙarin inganta gine-gine.

 

Kasafin kuɗin 2025 zai shafi gudanar da ayyukan filin jirgin sama na Gusau da kuma aikin gina hanyar Gusau-Magami zuwa Dansadau.

 

“Hakazalika, Kasafin 2025 zai shafi samar da kayan aikin tsaro ta hanyar ‘Asusun Tsaro’, gina makarantu ta hanyar shirin Agile, kafa cibiyar bincike ta zamani, gina birnin na zamani, samar da abinci a ƙarƙashin shirin Fadama III, sauƙin kasuwanci ta hanyar ‘Saber Program’, gyara Cibiyar Bafarawa Shinkafi, da gina Cibiyar Taro ta Duniya.

 

“Aikin gina titin Lalan zuwa Lalan, inganta asibitin ƙwararru na Yariman Bakura zuwa asibitin koyarwa, gina ƙarin gine-gine a manyan asibitocin Anka, Kauran namoda, Gummi, Shinkafi, Magami, Tsafe, Jangebe, da Bukkuyum, inganta wuraren kwanan ‘yan gudun hijira ta hanyar shirin Solid, haɓaka yawan amfani da dabbobi ta hanyar shirin L-Press, gina hanyar mai nisan kilomita 126 daga magami-dangulbi-dankurmi-bagega-anka.”

 

Sauran ayyukan da za a ƙaddamar a cikin kasafin kuɗin 2025 sun haɗa da shirin NG-Cares na ƙarfafa ci gaban al’umma, gina cibiyar wasanni ta Gusau, gina titin Mallamawa – Zarummai – Bukkuyyum, gina sabuwar makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta Zurmi, kammalawa Cibiyar Siyayya ta Gusau da ke tsohon wurin shaƙatawa, da kuma gina titin kilomita 94 a Yandoton Daji-Doka-Yanwaren-daji-Hayin alhaji-Bedi-Yankuzo-Tsafe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dakarun MNJTF Sun Daƙile Harin Da Aka Kai Sansanin Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10 A Kamaru

Next Post

Kasar Sin Na Adawa Da Danne Kamfanoninta Da Amurka Take Yi Bisa Fakewa Da Batun Tsaron Kasa

Related

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

1 hour ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

3 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

4 hours ago
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

13 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

15 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

16 hours ago
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Danne Kamfanoninta Da Amurka Take Yi Bisa Fakewa Da Batun Tsaron Kasa

Kasar Sin Na Adawa Da Danne Kamfanoninta Da Amurka Take Yi Bisa Fakewa Da Batun Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

July 1, 2025
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

July 1, 2025
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

July 1, 2025
Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.