• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Kudi Na Naira Biliyan 546 Na Shekarar 2025

by Sulaiman and Hussein Yero
10 months ago
Gwamna lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗin shekarar 2025 na Naira 546,014,575,000.00.

 

Kasafin kuɗin 2025 mai taken; “Kasafin Ceto 2.0”, kakakin majalisar dokokin jihar Zamfara ya gabatar wa gwamnan a ranar Alhamis a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau.

  • Dakarun MNJTF Sun Daƙile Harin Da Aka Kai Sansanin Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10 A Kamaru
  • Dubun Sojan Gona Ta Cika Bayan Damfarar Mutane A Jihar Yobe

A yayin rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2025, Gwamna Lawal ya ƙuduri aniyar kammala dukkan ayyukan da ake gudanarwa tare da inganta nasarorin da aka samu a cikin watanni 18 da gwamnatinsa ta yi.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

Gwamnan ya bayyana muhimmancin kasafin kuɗin shekarar 2025, inda ya ce ‘ba wai kawai mu kalli inda muke ko kuma inda muka dosa ba, amma inda muka kasance’.

 

“Abin ya tsananta a bara. Shekaru goma na rashin shugabanci nagari ya haifar da durƙushewar tattalin arziki, rashin biyan ma’aikatan gwamnati albashi, da kuma basussukan da ke kawo cikas ga ilimin yara. An lalata ababen more rayuwa, an yi watsi da asibitoci, kuma ayyukan jama’a sun ɗaiɗaita. Bugu da qari kuma, akwai rashin bin doka da oda, da batun kuɗin wutar lantarki da ake ci gaba da yi, da rashin isasshen ruwan sha, rashin tsaro, da ƙaruwar cututtuka masu yaɗuwa kamar kwalara, tare da raguwar kuɗaɗen shiga na cikin gida.

 

“Da ba mu yi gaggawar magance dukkan ƙalubalen ba, da jihar Zamfara ba za ta zama wurin da dukkan mu za mu iya rayuwa a yau ba.

 

“Ƙudirin Ceto na 2025 2.0 yana gudana ne ta hanyar jajircewarmu na ci gaba da ayyukan da muka fara wa mutanenmu, wanda ke nuna kyawawan manufofi na kishi. Wannan kasafin kuɗin kuma ya sanya aka ƙara wa ma’aikata ƙarin albashi mafi ƙaranci, inda ya tashi daga N30,000 zuwa N70,000.

 

Gwamna Lawal ya bayyana cewa lokaci ya yi da jihar Zamfara za ta shawo kan lalacewar ababen more rayuwa da kuma ƙoƙarin inganta gine-gine.

 

Kasafin kuɗin 2025 zai shafi gudanar da ayyukan filin jirgin sama na Gusau da kuma aikin gina hanyar Gusau-Magami zuwa Dansadau.

 

“Hakazalika, Kasafin 2025 zai shafi samar da kayan aikin tsaro ta hanyar ‘Asusun Tsaro’, gina makarantu ta hanyar shirin Agile, kafa cibiyar bincike ta zamani, gina birnin na zamani, samar da abinci a ƙarƙashin shirin Fadama III, sauƙin kasuwanci ta hanyar ‘Saber Program’, gyara Cibiyar Bafarawa Shinkafi, da gina Cibiyar Taro ta Duniya.

 

“Aikin gina titin Lalan zuwa Lalan, inganta asibitin ƙwararru na Yariman Bakura zuwa asibitin koyarwa, gina ƙarin gine-gine a manyan asibitocin Anka, Kauran namoda, Gummi, Shinkafi, Magami, Tsafe, Jangebe, da Bukkuyum, inganta wuraren kwanan ‘yan gudun hijira ta hanyar shirin Solid, haɓaka yawan amfani da dabbobi ta hanyar shirin L-Press, gina hanyar mai nisan kilomita 126 daga magami-dangulbi-dankurmi-bagega-anka.”

 

Sauran ayyukan da za a ƙaddamar a cikin kasafin kuɗin 2025 sun haɗa da shirin NG-Cares na ƙarfafa ci gaban al’umma, gina cibiyar wasanni ta Gusau, gina titin Mallamawa – Zarummai – Bukkuyyum, gina sabuwar makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta Zurmi, kammalawa Cibiyar Siyayya ta Gusau da ke tsohon wurin shaƙatawa, da kuma gina titin kilomita 94 a Yandoton Daji-Doka-Yanwaren-daji-Hayin alhaji-Bedi-Yankuzo-Tsafe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai
Labarai

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

October 26, 2025
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Danne Kamfanoninta Da Amurka Take Yi Bisa Fakewa Da Batun Tsaron Kasa

Kasar Sin Na Adawa Da Danne Kamfanoninta Da Amurka Take Yi Bisa Fakewa Da Batun Tsaron Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

Sin Da Amurka Sun Cimma Matsaya Dangane Da Tsare-Tsaren Warware Batutuwan Cinikayya Da Suke Mayar Da Hankali A Kai

October 26, 2025
Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Sharhi: Wannan Manufar Sin Za Ta Sa Kaimin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

October 26, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

Gwamnonin Arewa Sun Jajanta Wa Jihar Neja Kan Fashewar Tankar Mai

October 26, 2025
El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

El Classico: Abinda Ya Kamata Ku Sani Dangane Da Wasan Barcelona Da Real Madrid

October 26, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Masu Ƙananan Sana’o’i Biliyan 75 Domin Bunƙasa Kasuwancinsu

October 26, 2025
Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

Ɗan Majalisa Ya Ce Ba Zai Sake Takara Ba, Ya Sadaukar Da Ita Ga Matasa

October 26, 2025
Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

Abin Da Ya Sa Aka Yi Watsi Da Tashar Jiragen Ruwa Ta Kan Tudu Da Ke Jihar Kaduna

October 26, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutum Biyu Da Ake Zargi Da Haɗa Baki Da ‘Yan Bindiga A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwamnatin Kaduna Tare Da  AUDA–NEPAD Sun Tallafa Wa Manoma 400 Da Kayan Noma

October 26, 2025
Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

Tornadoes Ta Doke Pillars A Wasan Farko Na Babaganaru

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.