• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Ginin Birnin Fasaha Domin Horas Da Matasa 1,600 Duk Shekara 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Ginin Birnin Fasaha Domin Horas Da Matasa 1,600 Duk Shekara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya kaddamar da aikin gina birnin koyar da sana’o’i da fasaha a Rigachikun da ke karamar hukumar Igabi a jihar.

Ya ce, idan aka kammala cibiyar, za ta horas da matasa 400 duk bayan wata Uku-uku, a duk Shekara, za a horas da matasa 1,600 sana’o’i 19 daban-daban.

  • ‘Mutuwar Aminu S. Bono Ta Girgiza Kannywood’
  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

Da yake jawabi yayin kaddamar da ginin a ranar Asabar, Gwamnan ya ce za a sake gina irin birnin a duk fadin mazabun sanatoci uku na tarayya da ke jihar.

Gwamna Uba ya bayyana cewa, wannan kuduri na daga cikin tsarin gwamnatin tarayya na cike gibin da ake da shi a bangaren fasaha da koyar da sana’o’i a tsakanin matasa wanda gwamnatin ta himmatu wajen habbakawa daga kashi 23 zuwa 46 cikin 100 nan da shekarar 2030.

A cewarsa, “A lokacin yakin neman zabenmu, mun yi wa al’ummar jihar Kaduna alkawarin bunkasa ci gaban al’umma domin baiwa matasanmu ilimin fasaha da za su yi gogayya da takwarorinsu na duniya. Da yawan ayyukan da ya dace a baiwa mutanenmu na cikin gida amma sai a mikawa baƙi saboda ƙarancin fasaha. Don haka, mun gano akwai bukatar gaggawa na a sake horas da mutanenmu fasahohi da kirkire-kirkire don su zama abin nema wajen daukar ayyuka.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Birnin Fasaha
Gwamna Uba sani tare da Mataimakiyarsa, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe da Dan Majalisa Zailani a yayin a za tubalin ginin birnin Fasaha

“Wannan birnin kimiyya da fasaha na Jihar Kaduna da za a gina, za a horas da matasa a fanni daban-daban da ya hada da:

  • Takardar shaidar kwarewa a fannin Kwamfuta na kasa da kasa daga Microsoft Cisco.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin walda a bangaren man fetur da gas
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin tukin mota.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin firiji da na’urar sanyi (AC)
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin wutar lantarkin motoci.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin gyaran motoci
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin dafa abinci
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin walda
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin sanya dandamalin tayels
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin lantarki mai amfani da hasken rana.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin Aluminiyom
  • Takardar shaidar kwarewa a fanni Ado Da kwalliya.

Anasa jawabin, Sakataren zartarwa na hukumar kula da ilimin fasaha ta kasa (NBTE), Farfesa Idris Bugaje wanda Darakta a hukumar NBTE, Abbati Mohammed ya wakilta ya ce, wannan shiri na da matukar amfani ga raya matasa wanda hakan zai habbaka tattalin arzikin kasa. Don haka, Gwamna Uba Sani ya cancanci a yaba masa bisa jajircewarsa na gani al’umma ta ci gaba.

Birnin Fasaha

Ginin Birnin zai kasance kamar haka: Dakunan horaswa 16, Dakunan kwanan dalibai guda hudu, ajujuwa, ginin gudanarwar birnin, asibiti, wurin cin abinci, kantina, filin wasan kwallon kwando, filin wasan kwallon kafa, masallaci, dakin janareta, bandakuna da filin ajiye motoci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamna Uba SaniKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Yi Da Na Sanin Kalaman Da Na Furta Game Da Masana’antar Kannywood Ba -Amdaz

Next Post

Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

3 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

7 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

10 hours ago
Next Post
Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.