• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Ginin Birnin Fasaha Domin Horas Da Matasa 1,600 Duk Shekara 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Ginin Birnin Fasaha Domin Horas Da Matasa 1,600 Duk Shekara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya kaddamar da aikin gina birnin koyar da sana’o’i da fasaha a Rigachikun da ke karamar hukumar Igabi a jihar.

Ya ce, idan aka kammala cibiyar, za ta horas da matasa 400 duk bayan wata Uku-uku, a duk Shekara, za a horas da matasa 1,600 sana’o’i 19 daban-daban.

  • ‘Mutuwar Aminu S. Bono Ta Girgiza Kannywood’
  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

Da yake jawabi yayin kaddamar da ginin a ranar Asabar, Gwamnan ya ce za a sake gina irin birnin a duk fadin mazabun sanatoci uku na tarayya da ke jihar.

Gwamna Uba ya bayyana cewa, wannan kuduri na daga cikin tsarin gwamnatin tarayya na cike gibin da ake da shi a bangaren fasaha da koyar da sana’o’i a tsakanin matasa wanda gwamnatin ta himmatu wajen habbakawa daga kashi 23 zuwa 46 cikin 100 nan da shekarar 2030.

A cewarsa, “A lokacin yakin neman zabenmu, mun yi wa al’ummar jihar Kaduna alkawarin bunkasa ci gaban al’umma domin baiwa matasanmu ilimin fasaha da za su yi gogayya da takwarorinsu na duniya. Da yawan ayyukan da ya dace a baiwa mutanenmu na cikin gida amma sai a mikawa baƙi saboda ƙarancin fasaha. Don haka, mun gano akwai bukatar gaggawa na a sake horas da mutanenmu fasahohi da kirkire-kirkire don su zama abin nema wajen daukar ayyuka.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

Birnin Fasaha
Gwamna Uba sani tare da Mataimakiyarsa, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe da Dan Majalisa Zailani a yayin a za tubalin ginin birnin Fasaha

“Wannan birnin kimiyya da fasaha na Jihar Kaduna da za a gina, za a horas da matasa a fanni daban-daban da ya hada da:

  • Takardar shaidar kwarewa a fannin Kwamfuta na kasa da kasa daga Microsoft Cisco.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin walda a bangaren man fetur da gas
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin tukin mota.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin firiji da na’urar sanyi (AC)
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin wutar lantarkin motoci.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin gyaran motoci
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin dafa abinci
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin walda
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin sanya dandamalin tayels
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin lantarki mai amfani da hasken rana.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin Aluminiyom
  • Takardar shaidar kwarewa a fanni Ado Da kwalliya.

Anasa jawabin, Sakataren zartarwa na hukumar kula da ilimin fasaha ta kasa (NBTE), Farfesa Idris Bugaje wanda Darakta a hukumar NBTE, Abbati Mohammed ya wakilta ya ce, wannan shiri na da matukar amfani ga raya matasa wanda hakan zai habbaka tattalin arzikin kasa. Don haka, Gwamna Uba Sani ya cancanci a yaba masa bisa jajircewarsa na gani al’umma ta ci gaba.

Birnin Fasaha

Ginin Birnin zai kasance kamar haka: Dakunan horaswa 16, Dakunan kwanan dalibai guda hudu, ajujuwa, ginin gudanarwar birnin, asibiti, wurin cin abinci, kantina, filin wasan kwallon kwando, filin wasan kwallon kafa, masallaci, dakin janareta, bandakuna da filin ajiye motoci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamna Uba SaniKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Yi Da Na Sanin Kalaman Da Na Furta Game Da Masana’antar Kannywood Ba -Amdaz

Next Post

Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

Related

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

2 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

4 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

5 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

6 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

7 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

11 hours ago
Next Post
Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.