• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Ginin Birnin Fasaha Domin Horas Da Matasa 1,600 Duk Shekara 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Ginin Birnin Fasaha Domin Horas Da Matasa 1,600 Duk Shekara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani ya kaddamar da aikin gina birnin koyar da sana’o’i da fasaha a Rigachikun da ke karamar hukumar Igabi a jihar.

Ya ce, idan aka kammala cibiyar, za ta horas da matasa 400 duk bayan wata Uku-uku, a duk Shekara, za a horas da matasa 1,600 sana’o’i 19 daban-daban.

  • ‘Mutuwar Aminu S. Bono Ta Girgiza Kannywood’
  • Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Ministar Harkokin Wajen Faransa

Da yake jawabi yayin kaddamar da ginin a ranar Asabar, Gwamnan ya ce za a sake gina irin birnin a duk fadin mazabun sanatoci uku na tarayya da ke jihar.

Gwamna Uba ya bayyana cewa, wannan kuduri na daga cikin tsarin gwamnatin tarayya na cike gibin da ake da shi a bangaren fasaha da koyar da sana’o’i a tsakanin matasa wanda gwamnatin ta himmatu wajen habbakawa daga kashi 23 zuwa 46 cikin 100 nan da shekarar 2030.

A cewarsa, “A lokacin yakin neman zabenmu, mun yi wa al’ummar jihar Kaduna alkawarin bunkasa ci gaban al’umma domin baiwa matasanmu ilimin fasaha da za su yi gogayya da takwarorinsu na duniya. Da yawan ayyukan da ya dace a baiwa mutanenmu na cikin gida amma sai a mikawa baƙi saboda ƙarancin fasaha. Don haka, mun gano akwai bukatar gaggawa na a sake horas da mutanenmu fasahohi da kirkire-kirkire don su zama abin nema wajen daukar ayyuka.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Birnin Fasaha
Gwamna Uba sani tare da Mataimakiyarsa, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe da Dan Majalisa Zailani a yayin a za tubalin ginin birnin Fasaha

“Wannan birnin kimiyya da fasaha na Jihar Kaduna da za a gina, za a horas da matasa a fanni daban-daban da ya hada da:

  • Takardar shaidar kwarewa a fannin Kwamfuta na kasa da kasa daga Microsoft Cisco.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin walda a bangaren man fetur da gas
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin tukin mota.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin firiji da na’urar sanyi (AC)
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin wutar lantarkin motoci.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin gyaran motoci
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin dafa abinci
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin walda
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin sanya dandamalin tayels
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin lantarki mai amfani da hasken rana.
  • Takardar shaidar kwarewa a fannin aikin Aluminiyom
  • Takardar shaidar kwarewa a fanni Ado Da kwalliya.

Anasa jawabin, Sakataren zartarwa na hukumar kula da ilimin fasaha ta kasa (NBTE), Farfesa Idris Bugaje wanda Darakta a hukumar NBTE, Abbati Mohammed ya wakilta ya ce, wannan shiri na da matukar amfani ga raya matasa wanda hakan zai habbaka tattalin arzikin kasa. Don haka, Gwamna Uba Sani ya cancanci a yaba masa bisa jajircewarsa na gani al’umma ta ci gaba.

Birnin Fasaha

Ginin Birnin zai kasance kamar haka: Dakunan horaswa 16, Dakunan kwanan dalibai guda hudu, ajujuwa, ginin gudanarwar birnin, asibiti, wurin cin abinci, kantina, filin wasan kwallon kwando, filin wasan kwallon kafa, masallaci, dakin janareta, bandakuna da filin ajiye motoci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGwamna Uba SaniKaduna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ban Yi Da Na Sanin Kalaman Da Na Furta Game Da Masana’antar Kannywood Ba -Amdaz

Next Post

Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

5 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

8 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

9 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

11 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

12 hours ago
Next Post
Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

Na Yafe Wa Aminu S Bono Duka Kudaden Da Nake Bin Sa -Murja Kunya

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.