• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Gwangwaje ‘Yan Bijilante Da Miliyan 100

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Gwangwaje ‘Yan Bijilante Da Miliyan 100
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Bauchi ta bayar da kyautar naira miliyan 100 ga ƙungiyoyin ‘yan Bijilante da ‘yan Banga domin nuna godiya da jinjina kan irin kokarin da suke yi wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali musamman wajen kare dazukan da suke jihar daga aikace-aikacen ‘yan bindiga.

Gwamnan jihar Bala Muhammad shi ne ya sanar da wannan matakin a ranar Asabar lokacin da ya amshi bakwancin mambobi da shugabannin ƙungiyoyin ‘yan Bijilante da ‘yan Banga da suka kai masa ziyara ta musamman a gidan gwamnatin jihar.

  • Haaland Ya Zama Gwarzon Dan Wasan Duniya Na BBC A Bana
  • Gwagwarmayar Neman Takardar Naira: Ina Tsabar Kudin?

Gwamna Bala ya buƙaci ‘yan bijilante ɗin da su tabbatar da yin amfani da kuɗaɗen ta hanyoyin da suka dace tare da sayan kayayyakin da suka dace da za su taimaka musu wajen inganta ayyukansu.

Ya ce, tallafin zai ɗauki tsawon lokaci na taimaka musu wajen bada nasu gudunmawar wajen tabbatar da daƙile aikace-aikacen ta’addanci da ‘yan ta’adda a faɗin jihar.

A cewarsa, zaman lafiyan da jihar Bauchi ke mora, ya taimaka wajen janyo hankalin masu zuba hannun jari domin su zo jihar wajen zuba hannun jari a ɓangarori daban-daban na cigaban tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Gwamnan ya bayar da tabbacin gwamnatin jihar a ƙarƙashinsa na cigaba da taimaka wa hukumomin tsaro ciki har da ‘yan sa-kai wato ‘yan ƙato da gora domin kyautata zaman lafiya a jihar.

Ya ce, sabuwar ma’aikatar kula da tsaron cikin gida za ta cigaba da maida hankali wajen fito da tsare-tsaren da suka dace na kyautata zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin jihar.

A nasa ɓangaren, kwamanda janar na ƙungiyar mafarauta, Aliyu Umar Shayi, ya ce, ƙungiyarsa na aiki ƙungiyoyin ‘yan bijilante sama da 70 a sassa daban-daban na jihar da suke bada nasu gudunmawar wajen kyautata zaman lafiyan jihar.

Shayi ya nuna godiyarsu ga irin taimako da goyon bayan da gwamnan jihar ke basu wajen gudanar da nasu ayyukan yadda ya kamata a matsayinsu na ‘yan sa-kai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Haaland Ya Zama Gwarzon Dan Wasan Duniya Na BBC A Bana

Next Post

Manoma 40,000 Za Su Amfana Da Takin Zamani Na Bunkasa Noman Rani A Filato

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

48 minutes ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

4 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

6 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

8 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

9 hours ago
Next Post
Manoma 40,000 Za Su Amfana Da Takin Zamani Na Bunkasa Noman Rani A Filato

Manoma 40,000 Za Su Amfana Da Takin Zamani Na Bunkasa Noman Rani A Filato

LABARAI MASU NASABA

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.