• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Gwangwaje ‘Yan Bijilante Da Miliyan 100

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Gwamnatin jihar Bauchi ta bayar da kyautar naira miliyan 100 ga ƙungiyoyin ‘yan Bijilante da ‘yan Banga domin nuna godiya da jinjina kan irin kokarin da suke yi wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali musamman wajen kare dazukan da suke jihar daga aikace-aikacen ‘yan bindiga.

Gwamnan jihar Bala Muhammad shi ne ya sanar da wannan matakin a ranar Asabar lokacin da ya amshi bakwancin mambobi da shugabannin ƙungiyoyin ‘yan Bijilante da ‘yan Banga da suka kai masa ziyara ta musamman a gidan gwamnatin jihar.

  • Haaland Ya Zama Gwarzon Dan Wasan Duniya Na BBC A Bana
  • Gwagwarmayar Neman Takardar Naira: Ina Tsabar Kudin?

Gwamna Bala ya buƙaci ‘yan bijilante ɗin da su tabbatar da yin amfani da kuɗaɗen ta hanyoyin da suka dace tare da sayan kayayyakin da suka dace da za su taimaka musu wajen inganta ayyukansu.

Ya ce, tallafin zai ɗauki tsawon lokaci na taimaka musu wajen bada nasu gudunmawar wajen tabbatar da daƙile aikace-aikacen ta’addanci da ‘yan ta’adda a faɗin jihar.

A cewarsa, zaman lafiyan da jihar Bauchi ke mora, ya taimaka wajen janyo hankalin masu zuba hannun jari domin su zo jihar wajen zuba hannun jari a ɓangarori daban-daban na cigaban tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Gwamnan ya bayar da tabbacin gwamnatin jihar a ƙarƙashinsa na cigaba da taimaka wa hukumomin tsaro ciki har da ‘yan sa-kai wato ‘yan ƙato da gora domin kyautata zaman lafiya a jihar.

Ya ce, sabuwar ma’aikatar kula da tsaron cikin gida za ta cigaba da maida hankali wajen fito da tsare-tsaren da suka dace na kyautata zaman lafiya da kwanciyar hankali a faɗin jihar.

A nasa ɓangaren, kwamanda janar na ƙungiyar mafarauta, Aliyu Umar Shayi, ya ce, ƙungiyarsa na aiki ƙungiyoyin ‘yan bijilante sama da 70 a sassa daban-daban na jihar da suke bada nasu gudunmawar wajen kyautata zaman lafiyan jihar.

Shayi ya nuna godiyarsu ga irin taimako da goyon bayan da gwamnan jihar ke basu wajen gudanar da nasu ayyukan yadda ya kamata a matsayinsu na ‘yan sa-kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato
Labarai

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Next Post
Manoma 40,000 Za Su Amfana Da Takin Zamani Na Bunkasa Noman Rani A Filato

Manoma 40,000 Za Su Amfana Da Takin Zamani Na Bunkasa Noman Rani A Filato

LABARAI MASU NASABA

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura

November 7, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Malaman Makaranta 500 Aiki

November 7, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.