• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Sabbin Hadimai 173

by Sadiq
5 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Sabbin Hadimai 173
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da bai wuce ƙasa da shekaru biyu ya kammala wa’adin mulkinsa ba, Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya amince da naɗin sabbin hadimai 173.

Sabbin naɗe-naɗen sun haɗa da: manyan hadimai na musamman guda shida, manyan hadimai guda 60, hadimai na musamman guda 38, da kuma wasu hadimai 63.

  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina

Yawancin sabbin hadiman za su riƙa aiki ne a fannonin siyasa, hulɗa da jama’a, batutuwan fansho da na ma’aikata.

Mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Mukhtar Mohammed Gidado, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata a Bauchi.

Gidado, ya ce naɗin hadiman na da nufin kawo sabbin dabaru a cikin gwamnati tare da tabbatar da cewa gwamnati tana wakiltar buƙatu da muradun al’ummar Jihar Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ya bayyana sabbin hadiman a matsayin ƙwararru masu gogewa a fannoni daban-daban na shugabanci da siyasa.

Ya ƙara da cewa an zaɓi sabbin hadiman ne bisa cancanta, kuma an ɗora musu nauyin tabbatar da tsarin mulki da ya fi mayar da hankali kan jama’a.

Gwamna Bala Mohammed ya taya su murna tare da kira a gare su da su ɗauki sabbin muƙamansu a matsayin hanya ta hidimta wa jama’a, su kasance masu jajircewa da biyayya wajen cika burinsa na ci gaban jihar da inganta ayyukan gwamnati.

“Wannan gwamnati ta ƙudiri aniyar ɗorewa da nasarorin da aka cimma ta hanyar gina kyakkyawan tarihi na shugabanci nagari da haɗin kai,” in ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bala MohammedBauchiNaɗiSabbin Hadimai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

Next Post

Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana

Related

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

1 hour ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

2 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

4 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

6 hours ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

7 hours ago
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

18 hours ago
Next Post
Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana

Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.