• English
  • Business News
Tuesday, May 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Sabbin Hadimai 173

by Sadiq
3 weeks ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Sabbin Hadimai 173
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da bai wuce ƙasa da shekaru biyu ya kammala wa’adin mulkinsa ba, Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya amince da naɗin sabbin hadimai 173.

Sabbin naɗe-naɗen sun haɗa da: manyan hadimai na musamman guda shida, manyan hadimai guda 60, hadimai na musamman guda 38, da kuma wasu hadimai 63.

  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina

Yawancin sabbin hadiman za su riƙa aiki ne a fannonin siyasa, hulɗa da jama’a, batutuwan fansho da na ma’aikata.

Mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Mukhtar Mohammed Gidado, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata a Bauchi.

Gidado, ya ce naɗin hadiman na da nufin kawo sabbin dabaru a cikin gwamnati tare da tabbatar da cewa gwamnati tana wakiltar buƙatu da muradun al’ummar Jihar Bauchi.

Labarai Masu Nasaba

Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON

Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22

Ya bayyana sabbin hadiman a matsayin ƙwararru masu gogewa a fannoni daban-daban na shugabanci da siyasa.

Ya ƙara da cewa an zaɓi sabbin hadiman ne bisa cancanta, kuma an ɗora musu nauyin tabbatar da tsarin mulki da ya fi mayar da hankali kan jama’a.

Gwamna Bala Mohammed ya taya su murna tare da kira a gare su da su ɗauki sabbin muƙamansu a matsayin hanya ta hidimta wa jama’a, su kasance masu jajircewa da biyayya wajen cika burinsa na ci gaban jihar da inganta ayyukan gwamnati.

“Wannan gwamnati ta ƙudiri aniyar ɗorewa da nasarorin da aka cimma ta hanyar gina kyakkyawan tarihi na shugabanci nagari da haɗin kai,” in ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bala MohammedBauchiNaɗiSabbin Hadimai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

Next Post

Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana

Related

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya
Manyan Labarai

Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON

1 hour ago
Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22

2 hours ago
Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi
Labarai

Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi

11 hours ago
Kotu
Labarai

Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa

13 hours ago
Fahimtar Hakikanin kasar Sin
Labarai

Fahimtar Hakikanin kasar Sin

16 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara

17 hours ago
Next Post
Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana

Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana

LABARAI MASU NASABA

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON

May 20, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22

Gwamnatin Kano Ta Ƙara Wa’adin Mako Guda Kan Dakatar Da Fina-finai 22

May 20, 2025
Kasar Sin Na Adawa Da Kai Wa Fararen Hula Da Kayayyakin More Rayuwa Hari A Sudan

Kasar Sin Na Adawa Da Kai Wa Fararen Hula Da Kayayyakin More Rayuwa Hari A Sudan

May 19, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Bunkasa Duk Da Matsaloli Da Dama

Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Bunkasa Duk Da Matsaloli Da Dama

May 19, 2025
Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi

Gwamna Nasir Ya Naɗa Sabbin Sakatarori Na Ƙananan Hukumomi 21 A Kebbi

May 19, 2025
Hadin Gwiwa Bisa Daidaito Da Girmama Juna Tsakanin Sin Da Amurka Zai Samar Da Moriyar Juna

Hadin Gwiwa Bisa Daidaito Da Girmama Juna Tsakanin Sin Da Amurka Zai Samar Da Moriyar Juna

May 19, 2025
Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA

Yankin Taiwan Ba Shi Da Iko Ko Hujjar Halartar Taron WHA

May 19, 2025
Kotu

Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa

May 19, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15

May 19, 2025
Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600

Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600

May 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.