• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Yi Wa Fursunoni 96 Afuwa, Ya Bai Wa Kowa Kyautar Dubu 100

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Bauchi Ya Yi Wa Fursunoni 96 Afuwa, Ya Bai Wa Kowa Kyautar Dubu 100
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya yi wa fursunoni 96 aka daure kan laifuka daban-daban a gidajen gyaran hali a jihar afuwa.

Gwamnan ya ba su kyautar Naira dubu 100 kowannensu da nufin su yi amfani da kudin wajen neman sana’ar da za su yi idan sun koma cikin al’umma.

  • Wuraren Kiwo: Fulani Sun Yi Murna Da Matakin Shugaban Kasa – Ngelzarma
  • Ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa 2 Sun Mutu A Yayin Turmutsutsun Karɓar Abincin Tallafi

Gwamnan, wanda ya yi amfani da karfin ikon da doka sashe 212 (1) na kundin tsarin mulkin Nijeriya 1999 (da aka yi wa kwaskwarima) ya ba shi karkashin yin afuwa.

A yayin jawabinsa, gwamna ya ce, ya yi afuwar ne bisa shawarwari da kwamitin bayar da shawara kan yin afuwa na jihar ya yi, biyo bayan bibiyar zamantakewar fursunonin a gidan gyaran hali da kuma irin tuba da nadamar da suka yi kan laifukan da aka same su.

A cewar gwamnan, wadanda kwamitin ya yi la’akari da su wajen ganin an sake su sun hada da masu yawan shekaru, fursunoni masu dauke da cututtuka da ka iya yaduwa, da kuma wadanda aka yi musu daurin rai da rai amma sun shafe sama da shekaru sama da 10 a tsare tare da nuna nadama da ake da fatan za su kasance masu amfani idan suka koma cikin al’ummominsu.

Labarai Masu Nasaba

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sannan, gwamnan ya biya kudin tara da aka yanke wa wasu da nufin su samu fita daga daurewar da aka musu.

Sai dai a cewarsa, kwamitin ya yi fatali da bukatar wasu da suka aikata manyan laifuka, inda aka ki amincewa da fito da su.

Muhammad, ya hori wadanda ya sanya hannu aka sake su da su kasance mutane na kwarai kana su tabbatar ba su koma rayuwarsu na bayae da ya kai su ga shiga gidan yari ba.

“Kan halin da kasar nan ke ciki, kowane daga cikinku za a ba shi naira dubu 100, ina jan hankalinku da ku yi amfani da kudaden ta hanyar da ya dace. Kudin ba daga aljihuna ba ne, daga aljihun jiha ne.”

Gwamnan jihar ya bukaci babban jojin jihar da ta taka wa alkalai musamman alkalan da suke kananan kotuna da su daina yawan jibge mutane a gidajen yari kan wasu ‘yan laifukan da ba su kai a gungunta wa mutum rayuwarsa a gidan yari ba.

Shi kuma a jawabinsa, shugaban kwamitin yin afuwa kuma kwamishinan shari’a na Jihar Bauchi Hassan U. El-Yakub (SAN), ya ce gwamnan ya amince da fitar da kudi sama da naira miliyan bakwai domin biyan kudaden tara da kotuna suka yanke wa fursunonin kan laifukan da suka aikata.

Sannan, ya ce gwamnan ya kuma sake amincewa da fitar da wani kudi da yawan su ya kai Naira miliyan 13 da za a raba wa fursunonin da aka saki a matsayin tallafi da kudin mota domin su koma gidajensu domin ci gaba da kasance masu amfani a cikin al’umma.

“Kwamitin bayar da shawara kan afuwa ya amshi bukata daga wajen fursunoni 106 da suke rokon yafiyar gwamna. Amma kwamitinmu ya kai ziyara zuwa gidajen yari da suke Bauchi, Alkaleri, Azare, Bogoro, Burra, Darazo, Ningi, Zaki, Gamawa, Misau, Shira, Toro, Tafawa Balewa da Jama’are, inda aka karshe kwamitin ya amince da bukatar fursunoni 96 kuma cikin tausayawar gwamna ana gabatar masa ya amince.”

A nasu jawaban daban-daban kwanturolan hukumar kula da gidan yari a jihar Bauchi, Ali Bajoga, kwamishinan ‘yansanda na Jihar Bauchi Auwal Musa da sauran sun jinjina wa gwamnan bisa yin afuwar, sun kuma nuna hakan zai kara rage cunkoson da ake fama da shi a gidajen gyaran hali a jihar.

Wasu daga cikin fursunonin da aka sake su, sun nuna godiyarsu tare da daukar alkawarin ba za su sake komawa rayuwarsu ta baya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hedkwatar CDC Ta Afirka Ta Samu Yabo A Matsayin Babban Sakamakon Hadin Gwiwar BRI

Next Post

Ku Yi Amanna Da Tinubu, Matsalolin Zu Su Zo Karshe, inji Ministan Yaɗa Labarai

Related

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

10 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

11 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

12 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

13 hours ago
Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku
Tsaro

Rashin Imani Ne Kisan Mutane 63 Da Boko Haram Ta Yi A Borno – Atiku

15 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

17 hours ago
Next Post
Ku Yi Amanna Da Tinubu, Matsalolin Zu Su Zo Karshe, inji Ministan Yaɗa Labarai

Ku Yi Amanna Da Tinubu, Matsalolin Zu Su Zo Karshe, inji Ministan Yaɗa Labarai

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.