• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Nada Ibrahim Na BBC A Matsayin Shugaban Kafar Yada Labarai Na Gombe

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Nada Ibrahim Na BBC A Matsayin Shugaban Kafar Yada Labarai Na Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe ya amince da nadin Ibrahim Isa na Gidan Rediyon BBC a matsayin Babban Daraktan Kafar Yada Labarai ta Jihar Gombe (GMC).

Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ne ya sanar da amincewar gwamnan, yana mai cewa nadin na Ibrahim Isa, wadda ya fara aiki nan take, ya samo asali ne daga nagartattun halaye da kwarewarsa a fannin yaɗa labarai.

  • Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC
  • Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Kwamitin Asusun Samar Da Tallafin Tsaro

Ibrahim Isa, yana da kwarewar aikin jarida ta fiye da shekaru ashirin, hakan ya sa ya yi fice a matsayin dan jarida mai tura rahotanni, mai haɗa labaru da karanta su, kuma mai gudanar da shirye-shiryen talabijin kana manajan watsa labarai.

Duba da gogewa da kwarewarsa, ana sa ran Ibrahim Isa zai yi amfani da sabbin dabaru da hikimomi a Hukumar Yada Labarun ta Jihar Gombe don inganta harkokin yada labarai, kamar yadda kakakin gwamnan Malam Ismaila Uba Misilli ya nakalto.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa jagorancin Ibrahim Isa zai taimaka wajen bunkasar kafar yada labaran ta GMC da yi wa al’umma hidima ta hanyar samar musu sahihan labarai da suka dace.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Har ila yau, Gwamna Inuwa Yahayan ya amince da daga darajar Dakta Ishiyaku Babayo Ibrahim, daga matsayin babban mataimaki na musamman (SSA) kan hadin gwiwa da abokan huldar ci gaba zuwa mai ba da shawara na musamman kan wannan fanni.

Sanarwar hakan wacce Sakataren Gwamnatin Jihar ya sanar, ta ce an dauki matakin ne duba da irin nasarorin da Dr. Ibrahim ya cimma, da jajircewarsa na musamman da kuma tasirin da ya yi cikin ɗan kankanin lokaci daga nada shi a matsayin mai bada shawarar.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa daga darajarsa zuwa mukamin mai ba da shawara na musamman zai kara habaka shirye-shiryen hadin-gwiwa na jihar tare da kara kaimi wajen samar da kudade da tallafi daga bangarori daban-daban na ci gaba don ba da gudummawa ga jin dadi da ci gaban Jihar Gombe baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yunkurin Juyin Mulki: Yau Shekaru 48 Da Kisan Janar Murtala Ramat 

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Gaggauta Dakatar Da Ayyukan Soji

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

3 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

5 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

5 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

6 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

9 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

11 hours ago
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Gaggauta Dakatar Da Ayyukan Soji

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Gaggauta Dakatar Da Ayyukan Soji

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.