• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Nada Ibrahim Na BBC A Matsayin Shugaban Kafar Yada Labarai Na Gombe

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Gombe Ya Nada Ibrahim Na BBC A Matsayin Shugaban Kafar Yada Labarai Na Gombe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na jihar Gombe ya amince da nadin Ibrahim Isa na Gidan Rediyon BBC a matsayin Babban Daraktan Kafar Yada Labarai ta Jihar Gombe (GMC).

Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njodi, ne ya sanar da amincewar gwamnan, yana mai cewa nadin na Ibrahim Isa, wadda ya fara aiki nan take, ya samo asali ne daga nagartattun halaye da kwarewarsa a fannin yaɗa labarai.

  • Matsin Rayuwa: Magidanta 106 Suka Daina Kula Da Iyalansu A Gombe Cikin 2023 – NHRC
  • Gwamnan Zamfara Ya Kaddamar Da Kwamitin Asusun Samar Da Tallafin Tsaro

Ibrahim Isa, yana da kwarewar aikin jarida ta fiye da shekaru ashirin, hakan ya sa ya yi fice a matsayin dan jarida mai tura rahotanni, mai haɗa labaru da karanta su, kuma mai gudanar da shirye-shiryen talabijin kana manajan watsa labarai.

Duba da gogewa da kwarewarsa, ana sa ran Ibrahim Isa zai yi amfani da sabbin dabaru da hikimomi a Hukumar Yada Labarun ta Jihar Gombe don inganta harkokin yada labarai, kamar yadda kakakin gwamnan Malam Ismaila Uba Misilli ya nakalto.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa jagorancin Ibrahim Isa zai taimaka wajen bunkasar kafar yada labaran ta GMC da yi wa al’umma hidima ta hanyar samar musu sahihan labarai da suka dace.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

Har ila yau, Gwamna Inuwa Yahayan ya amince da daga darajar Dakta Ishiyaku Babayo Ibrahim, daga matsayin babban mataimaki na musamman (SSA) kan hadin gwiwa da abokan huldar ci gaba zuwa mai ba da shawara na musamman kan wannan fanni.

Sanarwar hakan wacce Sakataren Gwamnatin Jihar ya sanar, ta ce an dauki matakin ne duba da irin nasarorin da Dr. Ibrahim ya cimma, da jajircewarsa na musamman da kuma tasirin da ya yi cikin ɗan kankanin lokaci daga nada shi a matsayin mai bada shawarar.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana kwarin gwiwar cewa daga darajarsa zuwa mukamin mai ba da shawara na musamman zai kara habaka shirye-shiryen hadin-gwiwa na jihar tare da kara kaimi wajen samar da kudade da tallafi daga bangarori daban-daban na ci gaba don ba da gudummawa ga jin dadi da ci gaban Jihar Gombe baki daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yunkurin Juyin Mulki: Yau Shekaru 48 Da Kisan Janar Murtala Ramat 

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Gaggauta Dakatar Da Ayyukan Soji

Related

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

49 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

2 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

7 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

15 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

16 hours ago
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Gaggauta Dakatar Da Ayyukan Soji

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Gaggauta Dakatar Da Ayyukan Soji

LABARAI MASU NASABA

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.