• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Gombe Ya Nada Mai Rikon Safiyo-Janar Da Babban Jami’in Kididdiga

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Inuwa Ya Bukaci Musulmai Su Ci Gaba Da Habbaka Darussan Ramadana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya amince da nadin Zakari Isa Kwami a matsayin mai rikon mukamin Safiyo-Janar da Ibrahim Abubakar Dule a matsayin mai rikon kwarya na babban jami’in kididdiga na Jihar Gombe. 

 

Shugaban ma’aikata na jihar, Alhaji Bappayo Yahaya ne ya sanar da amincewar Gwamnan, yana mai bayyana cewa hakan ya biyo bayan ritayar da masu rike da mukaman biyu suka yi ne, kuma ya dace da ikon da aka bai wa gwamna a sashi na 208 karamin sashi (2c) na kundin tsarin mulkin Nijeriya da aka yi wa kwaskwarima.

  • Zaben Gwamnan Adamawa: Kotu Ta Kori Karar Da Binani Ta Kai INEC

Ya ce, sabbin nade-naden an yi su ne bisa la’akari da cancanta, aminci da sadaukar da kai da kuma kwarewar da suke da shi a aikin gwamnati, inda ya bukace su da su sanya irin wadannan halaye da kwarewa nasu wajen gudanar da ayyukan su a sabbin mukaman nasu.

 

Labarai Masu Nasaba

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sabon Mukaddashin Safiyo-Janar din Zakari Isa Kwami, ya yi karatun digirin sa a harkar safiyo a Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) Bauchi, kuma ya fara aiki ne a shekarar 2006 a matsayin jami’in filaye kuma ya yi rajista da kungiyar kwararrun safiyo-safiyo ta Nijeriya wato Surveyors’ Council of Nigeria (SURCON) a shekarar 2017. Ya rike mukamai daban-daban har ya kai matsayin babban safiyo na jiha.

 

A nasa bangaren, mukaddashin babban jami’in kididdigan na jiha, Ibrahim Abubakar Dule, ya yi digirin sa ne a jami’ar Abuja. Ya kuma fara aiki a Jihar Gombe ne a shekarar 2005 a matsayin magatakardan kungiyoyin hadin kai, inda ya yi ta samun karin girma har zuwa matsayin babban magatakardan kungiyoyin hadin kai, daga nan kuma ya koma ofishin kididdiga na Jihar Gombe a matsayin babban jami’in kididdiga.

 

Dukkanin nade-naden sun fara aiki ne daga ranar 6 ga wannan wata na Afrilun 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

ISWAP Ta Yi Garkuwa Da Ma’aikatan Jinkai 3 Da Masu Tsaro 2 A Borno

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Yi Dirar Mikiya Wurin Taro, Sun Kashe Shugaban Al’umma A Imo 

Related

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina
Labarai

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

7 hours ago
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi
Labarai

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

8 hours ago
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21
Labarai

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

10 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

15 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

16 hours ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

17 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Da Sojoji 2 A Jihar Benuwe

'Yan Bindiga Sun Yi Dirar Mikiya Wurin Taro, Sun Kashe Shugaban Al'umma A Imo 

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.