• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kano ya buɗe Cibiyar Hadda da Nazarin Alƙur’ani A Gidan Kwankwaso

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abba Yusuf ya buɗe Cibiyar Hadda da Nazarin Alƙur’ani, wadda aka raɗa wa suna Majidaɗi Institute for Qur’anic Research and Advancement (MIQRA).

An sadaukar da cibiyar ne ga mahaifin Kwankwaso, Musa Sale Kwankwaso. Kuma an gina cibiyar a gidan Kwankwaso da ke kan titin Miller Road, Kano.

  • Nasihar Kwankwaso Ga Angwaye Da Amaren Kano: Ku Guji Binciken Wayoyin Junanku
  • Shirin Bunƙasa Ilmi A Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida Ta Tura Dalibai 1001 Karatu Kasashen Waje

Sanarwar da Kakakin Yaɗa Labarai na Gwamnan Kano, Sanusi Bature ya fitar, ya ce, “Gwamna Abba ya yaba wa Sanata Rabi’u Kwankwaso dangane da wannan gagarimin tanadi da ya yi wa al’umma wajen bunƙasa ilmin addinin Musulunci.”

Gwamnan ya ce, an kafa cibiyar a daidai lokacin da ya dace, idan aka yi la’akari da yawan makarantun allo da na Islamiyya da ke faɗin jihar, waɗanda ke buƙatar a narkar da su cikin tsarin makarantun zamani, domin daƙile yadda almajirai ke ta gararamba kan tituna.

Gwamnan ya ƙara da cewa, Sanata Kwankwaso ya samu gagarimar nasarar ayyukan inganta rayuwar al’umma a lokacin mulkinsa, musamman wajen bunƙasa addinin Musulunci.

Labarai Masu Nasaba

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Ya bada misali da aikin katange dukkan maƙabartun cikin birnin Kano, gyaran masallatan Juma’a a faɗin jihar, gina makarantun Islamiyya a ƙananan hukumomi 44.

Sai dai kuma Abba ya nuna damuwa dangane da yadda Gwamnatin da ta shuɗe a Kano, ta ƙi ƙarasa sauran makarantun da Kwankwaso bai kammala ginawa kafin cikar wa’adin mulkin sa ba.

Saboda haka, Gwamna Abba ya yi alƙawarin ƙarasa makarantun, kuma ya bada umarni ga Ma’aikatar Ilmi ta fara tsare-tsaren fara ɗaukar ɗalibai domin fara zangon karatu.

Sanata Kwankwaso ya ce an kafa MIQRA domin ta riƙa horas da mahaddata Alƙur’ani maza da mata domin samun satifiket ɗin firamare da sakandare, ta yadda za su samu hanyar zarcewa makarantun gaba da sakandare da jami’o’i.

Ɗalibai daban-daban sun jinjina wa Kwankwaso da Gwamnan Kano dangane da wannan shiri mai albarka da aka gina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Abba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rike Iyayen Gida Masu Amana Na Daga Sirrin Samun Nasara A Kannyywood – Muhammadu Murtala

Next Post

Mutum 5 Sun Mutu Sakamakon Konewar Tankar Mai A Kwara

Related

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

2 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

6 hours ago
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

7 hours ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

9 hours ago
Next Post
Mutum 5 Sun Mutu Sakamakon Konewar Tankar Mai A Kwara

Mutum 5 Sun Mutu Sakamakon Konewar Tankar Mai A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.