• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf a ranar Asabar ya bai wa jami’an tsaro umarnin su gaggauta dakile matsalar fadan daba da sauran ayyukan bata gari wanda ke gurgunta zaman lafiya a wasu sassan Jihar.

‘Yan daba a cikin kwanaki biyu sun mayar da  kwaryar birnin Kano wuri mara tabbas ta fuskar rahotonnin fadace-fadace, kwace kwayoyin hannu da sauran kananan Laifuka.

  • Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles
  • Hijirar Shugaban Ma’aikatan Tarayya Da Manyan Sakatarori Daga Tsarin Fansho Na CPS

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne  a lokacin taron mako-mako na majalisar zartarwar da aka gudanar a dakin taron fadar Gwamnatin Kano.

Gwamnan Abba Kabir Yusuf ya bayyana damuwarsa kan  yawaitar bullar fadace-fadacen daba, inda ya tabbatar da cewa Gwamnati ba za ta zuba ido ana kallon wadannan ayyukan daban, na ci gaba da tada  hankulan jama’a tare da haramtawa tarin jama’a masu kokarin kiyaye doka ci gaba da samun kwanciyar hankali ba.

Ya Jaddada cewa Gwamnatin Kano  za ta ci gaba da hada hannu da hukumomin tsaro domin tabbatar  da kiyaye rayukan da dukiyoyin  al’umma a ko wane lokaci.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Kazalik, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bukaci alkalai da su guji sakin ‘yan daba, inda ya jadadda barazanar da hakan ke haifarwa ga  kwanciyar hankalin mazauna Kano, sannan ya bayyana muhimmancin gaggauta yanke hukunci kan wadanda ke gaban shari’a.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bai wa hukumomin tsaro umarnin  da su tabbatar da yin aiki kamar yadda doka ta tsara wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma da suke yi wa aiki, ya ja kunnensu da su tsaya iyakar da doka ta tsara musu.

A karshe Gwamnan ya bukaci jama’ar Kano da su ci gaba da gudanar da harkokinsu, inda ya ba su tabbacin Gwamnati za ta kara jajircewa wajen tabbatar da tsaro tare da bukatar ci gaba da bai wa wannan Gwamnati cikakken hadin kai da goyon baya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Next Post
Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.