• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf a ranar Asabar ya bai wa jami’an tsaro umarnin su gaggauta dakile matsalar fadan daba da sauran ayyukan bata gari wanda ke gurgunta zaman lafiya a wasu sassan Jihar.

‘Yan daba a cikin kwanaki biyu sun mayar da  kwaryar birnin Kano wuri mara tabbas ta fuskar rahotonnin fadace-fadace, kwace kwayoyin hannu da sauran kananan Laifuka.

  • Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles
  • Hijirar Shugaban Ma’aikatan Tarayya Da Manyan Sakatarori Daga Tsarin Fansho Na CPS

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne  a lokacin taron mako-mako na majalisar zartarwar da aka gudanar a dakin taron fadar Gwamnatin Kano.

Gwamnan Abba Kabir Yusuf ya bayyana damuwarsa kan  yawaitar bullar fadace-fadacen daba, inda ya tabbatar da cewa Gwamnati ba za ta zuba ido ana kallon wadannan ayyukan daban, na ci gaba da tada  hankulan jama’a tare da haramtawa tarin jama’a masu kokarin kiyaye doka ci gaba da samun kwanciyar hankali ba.

Ya Jaddada cewa Gwamnatin Kano  za ta ci gaba da hada hannu da hukumomin tsaro domin tabbatar  da kiyaye rayukan da dukiyoyin  al’umma a ko wane lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Kazalik, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bukaci alkalai da su guji sakin ‘yan daba, inda ya jadadda barazanar da hakan ke haifarwa ga  kwanciyar hankalin mazauna Kano, sannan ya bayyana muhimmancin gaggauta yanke hukunci kan wadanda ke gaban shari’a.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bai wa hukumomin tsaro umarnin  da su tabbatar da yin aiki kamar yadda doka ta tsara wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma da suke yi wa aiki, ya ja kunnensu da su tsaya iyakar da doka ta tsara musu.

A karshe Gwamnan ya bukaci jama’ar Kano da su ci gaba da gudanar da harkokinsu, inda ya ba su tabbacin Gwamnati za ta kara jajircewa wajen tabbatar da tsaro tare da bukatar ci gaba da bai wa wannan Gwamnati cikakken hadin kai da goyon baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaFadan DabaJami'an TsarokanoUmarni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

Next Post

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

55 minutes ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

5 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

6 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

16 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

18 hours ago
Next Post
Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.