• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
12 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Kano Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Kawo Karshen Fadan Daba A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf a ranar Asabar ya bai wa jami’an tsaro umarnin su gaggauta dakile matsalar fadan daba da sauran ayyukan bata gari wanda ke gurgunta zaman lafiya a wasu sassan Jihar.

‘Yan daba a cikin kwanaki biyu sun mayar da  kwaryar birnin Kano wuri mara tabbas ta fuskar rahotonnin fadace-fadace, kwace kwayoyin hannu da sauran kananan Laifuka.

  • Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles
  • Hijirar Shugaban Ma’aikatan Tarayya Da Manyan Sakatarori Daga Tsarin Fansho Na CPS

Gwamnan ya bayar da wannan umarni ne  a lokacin taron mako-mako na majalisar zartarwar da aka gudanar a dakin taron fadar Gwamnatin Kano.

Gwamnan Abba Kabir Yusuf ya bayyana damuwarsa kan  yawaitar bullar fadace-fadacen daba, inda ya tabbatar da cewa Gwamnati ba za ta zuba ido ana kallon wadannan ayyukan daban, na ci gaba da tada  hankulan jama’a tare da haramtawa tarin jama’a masu kokarin kiyaye doka ci gaba da samun kwanciyar hankali ba.

Ya Jaddada cewa Gwamnatin Kano  za ta ci gaba da hada hannu da hukumomin tsaro domin tabbatar  da kiyaye rayukan da dukiyoyin  al’umma a ko wane lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Kazalik, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bukaci alkalai da su guji sakin ‘yan daba, inda ya jadadda barazanar da hakan ke haifarwa ga  kwanciyar hankalin mazauna Kano, sannan ya bayyana muhimmancin gaggauta yanke hukunci kan wadanda ke gaban shari’a.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bai wa hukumomin tsaro umarnin  da su tabbatar da yin aiki kamar yadda doka ta tsara wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma da suke yi wa aiki, ya ja kunnensu da su tsaya iyakar da doka ta tsara musu.

A karshe Gwamnan ya bukaci jama’ar Kano da su ci gaba da gudanar da harkokinsu, inda ya ba su tabbacin Gwamnati za ta kara jajircewa wajen tabbatar da tsaro tare da bukatar ci gaba da bai wa wannan Gwamnati cikakken hadin kai da goyon baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaFadan DabaJami'an TsarokanoUmarni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Yi Wa Finidi George Kora Da Hali Daga Aikin Kocin Super Eagles

Next Post

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

8 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

10 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

11 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

11 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

15 hours ago
Next Post
Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

Ko Mbappe Zai Lashe Kofin Zakarun Turai Da Ballon d’Or A Real Madrid?

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.