• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kebbi Ya Bukaci Maniyyatan Jihar Da Su Kasance Jakadu Nagari

by Umar Faruk
2 years ago
Kebbi

Gwamna Nasir Idris, ya bukaci maniyyata aikin hajjin bana daga jihar Kebbi da su kasance jakadu nagari a tsawon zaman da suka yi a kasar Saudiyya yayin da suke gabatar da aikin hajjin bana.

 

Dakta Nasir Idris, ya bayar da wannan shawarar ne a lokacin da ya kai ziyarar bankwana da rukunin farko na maniyyata a sansanin alhazai da ke Birnin Kebbi, ya bayyana cewa, an san alhazan jihar da zama masu bin doka da oda, inda ya yi kira gare su da su kiyaye irin wannan dabi’a.

  • Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

Ya sanar da su cewa wannan shi ne karon farko da gwamnati mai ci ta shirya tsarin gudanar da aikin Hajji kuma ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin an gudanar da aikin jigilar mahajjata a filin jirgin sama na Sir Ahamadu da ke Birnin Kebbi amma hukumar ta aiyana cewa jirgin zai tashi ne a filin jirgin sama na Sakkwato.

 

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

Ya shawarci alhazai da su dauki irin wannan ci gaban a matsayin wani aiki na Allah inda ya ce shi ma zai yi aikin Hajjin bana tare da su don ba shi damar duba wuraren da ake bukatar gyara.

 

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa an kammala duk wani shiri na jin dadi da jin dadin alhazai a kasar Saudiyya, sai dai ana jiran isowarsu kasa mai tsarki. Haka kuma ya bukaci mahajjatan da su kara himma wajen yi wa shugabannin kasa addu’ar samun nasara tare da samun zaman lafiya da ci gaba a Nijeriya.

 

A nasa jawabin, Amirul Hajj na jihar Kebbi na bana, tsohon ministan harkokin cikin gida, Janar Muhammadu Magoro, ya shaida wa gwamnan cewa an samar da komai domin ganin an gudanar da aikin Hajji cikin sauki.

 

Janar Magoro ya sanar da cewa likitoci goma sha takwas da adadin ma’aikatan lafiya da suka dace za su raka maniyyatan zuwa Saudiyya domin kulawa da bukatunsu na lafiya. Ya kuma kara da cewa an kafa kwamitoci goma sha hudu don tabbatar da jin dadin alhazai.

 

Matan Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris, Hajiya Zainab Nasir da Hajiya Nafisa Nasir sun bukaci maniyyata da su yi addu’a ga jihar da kasar Nijeriya yayin da suke a kasa mai tsarki.

 

A nata jawabin, Hajiya Zainab ta ce jerin laccoci da shirye-shiryen fadakarwa da karawa juna sani da aka yi wa mahajjata an yi su ne domin su tsara dabi’u da tunaninsu ta yadda za su fahimci mahimmanci da abubuwan da ke tattare da aikin hajji.

 

Ta bayyana cewa gwamnati ta yi tanadin isassun wuraren kwana, tsarin ciyarwa, kayan aiki, tallafin magunguna da sauran kayan agaji da za su samu nasarar gudanar da aikin hajji.

 

A nata bangaren, Hajiya Nafisa, ta bukaci alhazai da su kula da kayansu, ta kuma shawarce su da su yi taka-tsan-tsan wajen yin musanyar kudade a lokacin zamansu a kasar Saudiyya.

 

“Ya kamata ku tabbatar kun bar darussan da aka koya daga shirye-shiryen fadakarwa da laccoci daban-daban su shafi halayenku da kyau yayin gabatar da addu’o’i ga jihar Kebbi da kasar Nijeriya baki daya,” in ji ta.

 

Da yake jawabi a madadin mahajjatan, Ahmad Galadima daga karamar hukumar Argungu ya godewa gwamnan bisa tsarin da ya dace na gudanar da aikin Hajji

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati
Labarai

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Next Post
An bankado Asirin Wasu Ma’aikatan Hukumar RMAFC Bisa Zargi Yin Kutse A Tsarin IPPIS

An bankado Asirin Wasu Ma'aikatan Hukumar RMAFC Bisa Zargi Yin Kutse A Tsarin IPPIS

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.