ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Hajjin Bana

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bukaci maniyyatan jihar zuwa Saudiyya su kasance masu biyayya da bin doka da oda, kuma su kasance jakadu na gari ga jihar da Nijeriya a yayin da suke ƙkasa mai tsarki. 

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a jiya yayin jawabin sa na bankwana ga maniyyatan jihar a hukumar jin dadin alhazai ta Jihar Gombe, “Yayin da kuke kasa mai tsarki, don Allah ku kasance jakadu nagari ga kanku, da al’ummarku, da kananan hukumominku, da Jihar Gombe dama Nijeriya, don mu yi alfahari da ku,” in ji shi.

ADVERTISEMENT
  • Hajjin Bana: Kashin Farko Na Maniyyatan Adamawa 475 Sun Sauka Saudiyya

Da yake kira ga maniyyatan su nesanta kansu daga duk wani abu da ka iya bata musu aikin na Hajji, ko taba mutuncin su ko na Jihar Gombe, Gwamna Inuwa ya tunatar da su cewa a kasa mai tsarki doka tana aiki ba sani ba sabo kan duk wadda aka kama da aikata laifi ko rashin gaskiya.

 

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

Da yake yi wa maniyyatan fatan gudanar da karbabben aikin Hajji, gwamnan ya karfafa su da su rika tambayar jagororinsu kan duk wani abu da ya shige mu su duhu. Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen ganin alhazan jihar sun yi aikin Hajji cikin natsuwa tun daga Nijeriya har zuwa kasa mai tsarki.

Hajjin Bana

Da yake tsokaci kan matsalolin rayuwa dana tattalin arziki da zamantakewar al’ummar kasar nan, Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci maniyatan su zage damtse wajen yin addu’o’in Allah ya samar wa kasar mafita.

 

Gwamnan ya kuma bukaci jami’an hukumomin alhazai a dukkan matakai su gudanar da ayyukan su cikin gaskiya da amana da kishin kasa don gudanar da aikin Hajjin cikin nasara.

 

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Gombe, Mai Martaba Sarkin Dukku, Haruna Abdulkadir Rasheed, ya yaba wa gwamnan bisa jajircewarsa na ganin an gudanar da aikin Hajji na bana cikin nasara.

 

Da yake jan hankalin alhazan jihar su maida hankali ga ibada maimakon sayen tsaraba, shugaban ya bukaci maniyyatan su ba da hadin kai ga jami’an aikin Hajji na jiha da na kasa don samun nasarar gudanar da aikin.

Hajjin Bana

A jawabinsa na maraba, babban sakataren hukumar Alhaji Sa’adu Hassan, ya yaba wa gwamnan bisa samar da ingantaccen masauki ga maniyyatan jihar a ƙasa mai tsarki.

 

Ya ce da farko jirgi mai daukar alhazai 350 aka tsara zai yi jigilar alhazan jihar, amma bisa jajircewar da gwamnan ya yi, yanzu an samar da jirgi mai daukan mutum 550 da zai tashi da sawun farko na maniyyatan jihar. Ya ce bayan tantance maniyyatan da aka lika sunayensu, za a fara jigilar mahajjatan gadan-gadan a gobe Laraba.

Hajjin Bana
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Next Post
Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

Gwamnoni Sun Mara Wa Matakin Tinubu Na Cire Tallafin Mai Baya

LABARAI MASU NASABA

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.