ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Kebbi Ya Bukaci Maniyyatan Jihar Da Su Kasance Jakadu Nagari

by Umar Faruk
3 years ago
Kebbi

Gwamna Nasir Idris, ya bukaci maniyyata aikin hajjin bana daga jihar Kebbi da su kasance jakadu nagari a tsawon zaman da suka yi a kasar Saudiyya yayin da suke gabatar da aikin hajjin bana.

 

Dakta Nasir Idris, ya bayar da wannan shawarar ne a lokacin da ya kai ziyarar bankwana da rukunin farko na maniyyata a sansanin alhazai da ke Birnin Kebbi, ya bayyana cewa, an san alhazan jihar da zama masu bin doka da oda, inda ya yi kira gare su da su kiyaye irin wannan dabi’a.

ADVERTISEMENT
  • Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

Ya sanar da su cewa wannan shi ne karon farko da gwamnati mai ci ta shirya tsarin gudanar da aikin Hajji kuma ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin an gudanar da aikin jigilar mahajjata a filin jirgin sama na Sir Ahamadu da ke Birnin Kebbi amma hukumar ta aiyana cewa jirgin zai tashi ne a filin jirgin sama na Sakkwato.

 

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya shawarci alhazai da su dauki irin wannan ci gaban a matsayin wani aiki na Allah inda ya ce shi ma zai yi aikin Hajjin bana tare da su don ba shi damar duba wuraren da ake bukatar gyara.

 

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa an kammala duk wani shiri na jin dadi da jin dadin alhazai a kasar Saudiyya, sai dai ana jiran isowarsu kasa mai tsarki. Haka kuma ya bukaci mahajjatan da su kara himma wajen yi wa shugabannin kasa addu’ar samun nasara tare da samun zaman lafiya da ci gaba a Nijeriya.

 

A nasa jawabin, Amirul Hajj na jihar Kebbi na bana, tsohon ministan harkokin cikin gida, Janar Muhammadu Magoro, ya shaida wa gwamnan cewa an samar da komai domin ganin an gudanar da aikin Hajji cikin sauki.

 

Janar Magoro ya sanar da cewa likitoci goma sha takwas da adadin ma’aikatan lafiya da suka dace za su raka maniyyatan zuwa Saudiyya domin kulawa da bukatunsu na lafiya. Ya kuma kara da cewa an kafa kwamitoci goma sha hudu don tabbatar da jin dadin alhazai.

 

Matan Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris, Hajiya Zainab Nasir da Hajiya Nafisa Nasir sun bukaci maniyyata da su yi addu’a ga jihar da kasar Nijeriya yayin da suke a kasa mai tsarki.

 

A nata jawabin, Hajiya Zainab ta ce jerin laccoci da shirye-shiryen fadakarwa da karawa juna sani da aka yi wa mahajjata an yi su ne domin su tsara dabi’u da tunaninsu ta yadda za su fahimci mahimmanci da abubuwan da ke tattare da aikin hajji.

 

Ta bayyana cewa gwamnati ta yi tanadin isassun wuraren kwana, tsarin ciyarwa, kayan aiki, tallafin magunguna da sauran kayan agaji da za su samu nasarar gudanar da aikin hajji.

 

A nata bangaren, Hajiya Nafisa, ta bukaci alhazai da su kula da kayansu, ta kuma shawarce su da su yi taka-tsan-tsan wajen yin musanyar kudade a lokacin zamansu a kasar Saudiyya.

 

“Ya kamata ku tabbatar kun bar darussan da aka koya daga shirye-shiryen fadakarwa da laccoci daban-daban su shafi halayenku da kyau yayin gabatar da addu’o’i ga jihar Kebbi da kasar Nijeriya baki daya,” in ji ta.

 

Da yake jawabi a madadin mahajjatan, Ahmad Galadima daga karamar hukumar Argungu ya godewa gwamnan bisa tsarin da ya dace na gudanar da aikin Hajji

Kebbi
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Nijeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Sassauta Tsanantawa A Kan Iyakokinsu Ga ‘Yan Kasuwa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
An bankado Asirin Wasu Ma’aikatan Hukumar RMAFC Bisa Zargi Yin Kutse A Tsarin IPPIS

An bankado Asirin Wasu Ma'aikatan Hukumar RMAFC Bisa Zargi Yin Kutse A Tsarin IPPIS

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.