• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Biya ‘Yan Fansho Hakkokinsu Fiye Da Nb7

by Leadership Hausa
1 year ago
zamfara

Gwamna Dauda Lawal ya samu nasarar biyan haƙƙoƙin ‘yan fansho na Jihar Zamfara da na ƙananan hukumomi, fiye Naira Biliyan 7.

A watan Janairun wannan shekarar ne gwamnatin jihar Zamfara ta kafa wani kwamitin da zai tantance tsaffin ma’aikatan jihar da ba a biya su haƙƙin su na barin aiki ba, a tsakanin shekarar 2015 da 2024, da kuma bashin fanshon tsaffin ma’aikatan Ƙananan Hukumomi na tsakanin shekarar 2012 da 2019.

A cikin sanarwar da ya fitar yau a Gusau, Kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya bayyana cewa ya zuwa yanzu an samu nasarar biyan bashin kuɗi N7,345,674,918.42 a biya bakwai da aka yi.

Sanarwar ta Sulaiman Bala ta ƙara haske da cewa wannan aiki na biyan basussukan tsaffin ma’aikatan, yana tafiya ba tare da wata tangarɗa ba.

  • Zanga-zanga: Gwamnati Ta Sanya Dokar Hana Zirga-zirga Ta Awa 24 A Kano

 

LABARAI MASU NASABA

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Ya ce, “Gwamnatin jihar Zamfara a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta jajirce don ganin ta kammala biyan bashin tsaffin ma’aikatan jihar da na Ƙananan Hukumomi, wanda ya zarta Naira Biliyan 13.

“Abin takaici ne yadda gwamnatocin da suka gabata su ka bar tsaffin ma’aikatan cikin mawiyacin hali na ƙin biyan su haƙƙokin su na barin aiki, wanda alhamdu lillahi, yanzu Gwamna Lawal yana sallamar su.

“Yanzu dai waɗanda aka tantance su 1,926 cikin mutum 3,880 an biya su haƙƙoƙin su a biya bakwai da aka yi, wato kashi 1, 2, 3, 4, 5, da na 6, an biya su abin da ya kai ma tsabar kuɗi har N3,345,642,807.22, daga cikin N8,095,948,906.63 da ake bi.

“Kwanan nan ne aka biya kashi na bakwai, waɗanda suka kai su 215, wanda ya kai ma N499,886,578.77.

“A ɗaya ɓangaren kuma, an biya tsaffin ma’aikatan Ƙananan Hukumomi da Malaman makarantun Firamare su 3,513 a kashi bakwai, wanda ya kai ma N3,500,145,532.43.

“Za a ci gaba da wannan ƙoƙari, domin yana daga cikin shirin gwamnatin Zamfara na inganta harkar aikin gwamnati a jihar, don samar da ingantaccen aikin gwamnati.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Next Post
Ɓata-gari Sun Cinna Wa Sakatariyar APC Wuta Tare Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Jigawa

Ɓata-gari Sun Cinna Wa Sakatariyar APC Wuta Tare Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.