• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Biya ‘Yan Fansho Hakkokinsu Fiye Da Nb7

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Biya ‘Yan Fansho Hakkokinsu Fiye Da Nb7
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal ya samu nasarar biyan haƙƙoƙin ‘yan fansho na Jihar Zamfara da na ƙananan hukumomi, fiye Naira Biliyan 7.

A watan Janairun wannan shekarar ne gwamnatin jihar Zamfara ta kafa wani kwamitin da zai tantance tsaffin ma’aikatan jihar da ba a biya su haƙƙin su na barin aiki ba, a tsakanin shekarar 2015 da 2024, da kuma bashin fanshon tsaffin ma’aikatan Ƙananan Hukumomi na tsakanin shekarar 2012 da 2019.

A cikin sanarwar da ya fitar yau a Gusau, Kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya bayyana cewa ya zuwa yanzu an samu nasarar biyan bashin kuɗi N7,345,674,918.42 a biya bakwai da aka yi.

Sanarwar ta Sulaiman Bala ta ƙara haske da cewa wannan aiki na biyan basussukan tsaffin ma’aikatan, yana tafiya ba tare da wata tangarɗa ba.

  • Zanga-zanga: Gwamnati Ta Sanya Dokar Hana Zirga-zirga Ta Awa 24 A Kano

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Ya ce, “Gwamnatin jihar Zamfara a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta jajirce don ganin ta kammala biyan bashin tsaffin ma’aikatan jihar da na Ƙananan Hukumomi, wanda ya zarta Naira Biliyan 13.

“Abin takaici ne yadda gwamnatocin da suka gabata su ka bar tsaffin ma’aikatan cikin mawiyacin hali na ƙin biyan su haƙƙokin su na barin aiki, wanda alhamdu lillahi, yanzu Gwamna Lawal yana sallamar su.

“Yanzu dai waɗanda aka tantance su 1,926 cikin mutum 3,880 an biya su haƙƙoƙin su a biya bakwai da aka yi, wato kashi 1, 2, 3, 4, 5, da na 6, an biya su abin da ya kai ma tsabar kuɗi har N3,345,642,807.22, daga cikin N8,095,948,906.63 da ake bi.

“Kwanan nan ne aka biya kashi na bakwai, waɗanda suka kai su 215, wanda ya kai ma N499,886,578.77.

“A ɗaya ɓangaren kuma, an biya tsaffin ma’aikatan Ƙananan Hukumomi da Malaman makarantun Firamare su 3,513 a kashi bakwai, wanda ya kai ma N3,500,145,532.43.

“Za a ci gaba da wannan ƙoƙari, domin yana daga cikin shirin gwamnatin Zamfara na inganta harkar aikin gwamnati a jihar, don samar da ingantaccen aikin gwamnati.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan FanshoGwamna Dauda LawalZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kashe Yuan Biliyan 300 A Aikin Gina Tituna A Xizang A Tsakanin Shekarar 1953-2023

Next Post

Ɓata-gari Sun Cinna Wa Sakatariyar APC Wuta Tare Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Jigawa

Related

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

60 minutes ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

3 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

4 hours ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

6 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

7 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

7 hours ago
Next Post
Ɓata-gari Sun Cinna Wa Sakatariyar APC Wuta Tare Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Jigawa

Ɓata-gari Sun Cinna Wa Sakatariyar APC Wuta Tare Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Jigawa

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.