• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada

Ya sha alwashin hukunta waɗanda suka kashe Malamin 

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal, ya ziyarci garin Mada domin yin ta’aziyyar rasuwar babban Limamin garin, Marigayi Sheikh Abubakar Mada.

Idan za a iya tunawa, wasu da ake zargin ’yan banga ne suka kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada a makon jiya a garin Mada da ke Ƙaramar Hukumar Gusau ta Jihar Zamfara.

  • Xi Ya Halarci Zama Na Biyu Na Taron Shekara Shekara Na Majalisar NPC
  • Yadda Rayuwata Ta Sauya Bayan Mayar Da Tsintuwar Naira Miliyan 15 – Auwalu

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa Gwamna Lawal ya yi sallar Juma’a ne a masallacin garin Mada.

A cewar sanarwar, Gwamnan ya miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayi Sheikh Abubakar Hassan Mada, Hakimin gundumar, da sauran al’ummar yankin.

A yayin jawabinsa ga jama’a bayan sallar Juma’a, Gwamna Lawal ya yi alƙawarin yin duk mai yiwuwa don ganin an yi adalci a kan lamarin.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

“Na zo nan ne domin in tabbatar wa mutanen garin Mada cewa gwamnatina ta himmatu wajen ganin an tabbatar da adalci, tare da hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.

“Babu wani abu da za a bari wajen ganin an tabbatar da adalci a kan kisan Sheikh Abubakar. Za mu yi aiki tuƙuru don ganin cewa marigayi Sheikh da iyalansa sun samu adalcin da ya kamata,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta nakalto gwamnan yana cewa, “Bana Gusau lokacin da lamarin ya faru, amma bayan na samu wannan labari mai tada hankali, nan take na tuntuɓi shugabannin hukumomin tsaro da abin ya shafa a jihar domin ɗaukar matakin da ya dace”.

“’Yansanda sun fara gudanar da bincike cikin gaggawa kan kisan gillar. Na rantse da Allah za mu tabbatar da cewa duk wanda aka samu da laifi a wannan ɗanyen aikin, za a hukunta shi,” in ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Garin MadaKisan gillaMalamiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Halarci Zama Na Biyu Na Taron Shekara Shekara Na Majalisar NPC

Next Post

Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023

Related

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

46 minutes ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

1 hour ago
Zamfara
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

4 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

4 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

5 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

5 hours ago
Next Post
Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023

Kungiyar Lauyoyi Ta Tabbatar Da Fara Gurfanar Da Masu Laifukan Zaben 2023

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Zamfara

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Zamfara

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.