• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa

by Sulaiman
5 months ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Sabon Kwamishina Tare Da Yin Garambawul Ga Muƙarrabansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya yi garambawul a gwamnatinsa, sannan ya rantsar da wani sabon Kwamishina.

 

A Litinin ɗin nan ne Gwamna Dauda Lawal ya jagoranci zaman majalisar zartarwar jihar, inda a lokacin zaman ya rantsar da wani sabon Kwamishina.

  • Kamfanin Turkiyya Ya Fara Aikin inganta Noman Zamani A Zamfara 
  • Kebbi Da Brazil Zasu Yi Haɗin Gwuiwa Kan Sarrafa Nama Ta Hanyar Zamani

A cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa a wannan zaman Majalisar, gwamnan ya canja wa wasu Kwamishinoni wuraren aiki.

Sanarwar ta ce, an naɗa sabon Kwamishinan, Kasimu Sani Kaura ne don ya maye girbin Mannir Muazu Haidara, wanda ya ajiye aiki, kuma aka zaɓe shi a matsayin Shugaban Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda.

Labarai Masu Nasaba

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

Gwamna Lawal ya bayyana wa Majalisar cewa dacewa ce ta sa aka zaɓo Kasimu Sani Kaura don ya wakilci al’ummar Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda a Majalisar, wanda kuma ya kasance mutum ne jajirtacce game da ci gaban al’ummarsa, da ma jihar baki ɗaya.

Gwamnan ya ce, “Wannan naɗi, wata alamar tabbaci ce ta gwamnatin nan na zaƙulo jajirtattun mutanen da za su bayar da gagarumar gudumawa wajen inganta rayuwar al’umma da ci gaban jihar Zamfara.

“Ina mai yin kira ga sabon Kwamishinan kan ya bayar da rayuwarsa wajen yi wa al’ummar sa hidima. A matsayin sa na mamba a harkar ceto jihar Zamfara, ba ni da shakkun irin gagarumar gudumawar da zai bayar don amfanin jama’a.

“Mai girma Kwamishina, ina taya ka murnar wannan kira da aka yi maka don ka yi wa al’umma hidama. Ina maka, tare da dukkan mu fatan tsarewar Allah. Ina mai kira gare ka da ka kasance kana aiki kafaɗa da kafaɗa tare da sauran Kwamishinoni, da kuma ma’aikatan ma’aikatarka.

Gwamnan ya ce, ya lura da yadda dukkan muƙarrabansa ke gudanar da ayyukansu, wanda hakan ne ta sa ya yi wasu ‘yan canje-canje. “Don ganin mun samu nasarar sauke nauyin da ke kanmu, ina ganin akwai buƙatuwar yin wasu ‘yan canje-canje a gwamnatina.”

“Wannan sabon Kwamishina, Kasimu Sani Kaura, zai kula da ma’aikatar muhalli da albarkatun ƙasa, inda ya maye gurbin Hon. Mahmud Mohammed Abdullahi, Wanda aka mayar da shi mai kula da ma’aikatar yaɗa labarai da al’adu.

“Hon. Nasiru Ibrahim Zurmi kuma ya koma Kwamishina a ma’aikatar kula da birane, inda ya maye gurbin Hon. Kabiru Moyi, wanda ya koma. Ma’aikatar sanya ido da aiwatar da ayyuka.

“Bugu da ƙari, an canja Dr. Nafisa Muhammad zuwa ma’aikatar lafiya, inda ta maye gurbin Dr. Aisha M. Za Anka, wacce ta koma Kwamishina a ma’aikatar kula da mata da inganta jin daɗin jama’a.

“Za a kammala duk wasu shirye-shiryen miƙa shugabancin a tsakanin kwanaki bakwai. Ina so in ƙara tunatar da ku cewa zan ci gaba da sanya ido da yadda kuke gudanarwa, tare da auna ayyukanku, domin muna fuskantar rabin wa’adinmu a ofis. Mu yi amfani da wannan dama wajen jajircewa da sadaukarwa wajen yi wa jihar mu ta Zamfara hidima.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LakurawaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Inuwar Gamji

Next Post

Jagororin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam’iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

Related

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

4 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

5 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

6 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

7 hours ago
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

15 hours ago
Next Post
Jagororin Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam’iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

Jagororin Jam'iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin Sun Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki Da Ayyukan Jam'iyya Da Yaki Da Cin Hanci Na 2025

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.