ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Turkiyya Ya Fara Aikin inganta Noman Zamani A Zamfara 

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Noman zamani

Wani fitaccen kamfanin ƙasar Turkiyya mai suna Direkci zai fara aikin samar da na’urorin zamani a harkar noma tare da samar da lambunan zamani domin bunƙasa noma a Jihar Zamfara.

 

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne, Nurullah Mehmet, Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Gudanarwa na cibiyar Direkci, ya jagoranci tawagar da suka kai wa Gwamna Dauda Lawal ziyarar aiki a ofishinsa a gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Babu Uziri A Yaki Da Cin Zarafin Mata – Mohamed M. Fall
  • Shettima Ya Yaba Wa BUK Kan Bai Wa Dalibai Guraben Karatu Cikin Adalci

Kamfanin na ƙasar Turkiyya na shirin kawo sauyi a harkar noma a Jihar Zamfara ta hanyar noman auduga, da raƙe, da waken soya mai tarin yawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Baya ga noman gargajiya, cibiyar za ta bullo da hanyoyin noma na zamani, gami da amfani da fasaha wajen samar da lambuna da kiwon kaji, waɗanda za su ƙara inganta fannoni da dama a jihar.

 

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatin sa na tabbatar da samar da abinci da samar da ayyukan yi ga al’ummar Jihar Zamfara.

 

“Kamar yadda na yi alƙawari a lokacin yaƙin neman zabe, idan aka zabe ni, gwamnatina za ta mai da hankali kan tsaro, noma da samar da abinci, ilimi, kiwon lafiya, tattalin arziki, da ƙarfafawa al’umma.

 

“An san al’ummarmu a jihar Zamfara da noma. Burin mu shi ne mu farfaɗo da wannan fanni. Muna da burin tabbatar da tsaron jihar domin mutane su koma gonakinsu.

 

“Abu mai muhimmanci shi ne, bayan tabbatar da tsaro a gonaki, mataki na gaba shi ne samar da na’urorin zamani ga manoman mu, kasancewar mun riga mun sami filaye da ma’aikata.

 

“Wannan shi ne dalilin da ya sa muke maraba da haɗin gwiwar masu zuba jari irin su Direkci.

 

“Na yi tafiya zuwa Turkiyya a watan Yuli, inda na ziyarci ayyukan gonaki, kiwo, ayyukan kiwon kaji, da kuma masana’antar sarrafa na’urorin ayyukan noma ta Turk. Cibiyar Direkci ta zo Zamfara ne domin bullo da ci gaban fasaha a harkar noma.”

 

A farko, Nurullah Mehmet, Manajan Darakta kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Direkci, ya yaba wa Gwamna Lawal bisa ɗimbin ayyukan da gwamnatinsa ta fara a cikin ƙanƙanin lokaci.

 

“Kamfanin mu Direkci yana gudanar da ayyuka da dama a jihohi daban-daban na Nijeriya.

 

“Shirin noma na Direkci a jihar Zamfara zai inganta darajar noma tare da jawo zuba jari, da bunƙasa tattalin arzikin cikin gida.

 

“Shigo da lambunan zamani zai habaka noma a duk shekara, wajen kare amfani gona daga fari da sauran abubuwa.

 

“Noman zamani da na kiwon kaji za su samar da guraben aikin yi a matakai daban-daban, daga ma’aikatan gona zuwa ƙwararru a harkar noma.”

Noman zamani
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Noman zamani
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi Jami’anta Kan Rubutu A Kafafen Sadarwa 

Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi Jami'anta Kan Rubutu A Kafafen Sadarwa 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.