• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Shugaban Hukumar Zaɓen Jihar

Abubuwan Da Suka Wakana A Taron Majalisar Zartarwa Na Makon Nan

byLeadership Hausa
12 months ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya rantsar da Honarabul Bala Aliyu Gusau a matsayin Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) a wani ɓangare na shirye-shiryen gwamnatinsa gabanin zaɓen ƙananan hukumomi.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a ranar Litinin a yayin taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara a zauren majalisar da ke gidan gwamnati a Gusau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa wa’adin manyan shugabannin riƙo na ƙananan hukumin su 14 zai ƙare ne a ranar 23 ga Oktoba, 2024.

  • Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa, babbar Alƙalin jihar, Mai Shari’a Kulu Aliyu, wacce Mai Shari’a Mukhtar Yusha’u ya wakilta ta rantsar da Shugaban Hukumar Zaɓen.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

Har ila yau, Gwamna Lawal ya sanar da mambobin majalisar zartarwar jihar yayin zamanta cewa halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 79 da ya yi na da matuƙar amfani.

Ya bayyana fatan hakan zai haifar da sakamako mai kyau a ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar al’ummar Zamfara.

Gwamnan ya ce, ya sanya hannu kan gyaran dokar zaɓe ta jihar Zamfara makwannin da suka gabata gabanin zaɓen ƙananan hukumomin da ke tafe.

Ya ce, “A bisa hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke a kwanan baya game da zaben ƙananan hukumomi, muna buƙatar mu gudanar da zabe a ƙananan hukumomin mu cikin aminci.

“A bisa ga rattaba hannu kan dokar da aka yi wa kwaskwarima, hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar za ta sanar da jadawalin zaben da wuri-wuri domin mu samu zababbun shugabannin ƙananan hukumomi a Jihar Zamfara.

 

“Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) za ta fito da tsare-tsare kan zaɓen, kuma ana sa ran dukkanmu za mu ba da goyon baya da haɗin kan da ya dace domin samun nasarar aikin.”

Bugu da ƙari, a yayin taron majalisar, Gwamna Lawal ya umurci Sakataren gwamnatin jiha da ya haɗa hannu da mataimakin gwamnan domin gaggauta shirya bikin ƙaddamar da Hukumar Bunƙasa Zuba Jari ta Jihar Zamfara (ZIPA) domin ta yi aiki yadda ya kamata.

zamfarazamfara

Gwamnan ya kuma sanar da majalisar cewa jihar a shirye take ta fara aikin rabon kuɗi na ‘NG-Cares’.

“Aikin zai ttallafa wa marasa galihu, matasa marasa aikin yi da mata a faɗin ƙananan hukumomi 14 na jihar. Za a kashe jimillar kuɗi kusan Naira Biliyan 4.9.

“Masu cin gajiyar wannan shiri za su kasance mutane 5000 na matalauta da marasa galihu; ɗaukar matasa da mata marasa aikin yi 6000; tallafin inganta rayuwa rayuwa ga matasa da mata 8000.

“Dole ne mu yi adalci da nuna jagoranci nagari ga dukkan al’ummar jiharmu,” in ji shi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Mutane Kalilan Ne Suka Sace Dukiyar Nijeriya Ta Hanyar Tallafin Mai – Tinubu 

Ban Ji Dadin Abin Da Libya Ta Yi Wa Super Eagles Ba - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version