ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Rantsar Da Shugaban Hukumar Zaɓen Jihar

Abubuwan Da Suka Wakana A Taron Majalisar Zartarwa Na Makon Nan

by Leadership Hausa
2 years ago
zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya rantsar da Honarabul Bala Aliyu Gusau a matsayin Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) a wani ɓangare na shirye-shiryen gwamnatinsa gabanin zaɓen ƙananan hukumomi.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a ranar Litinin a yayin taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara a zauren majalisar da ke gidan gwamnati a Gusau.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa wa’adin manyan shugabannin riƙo na ƙananan hukumin su 14 zai ƙare ne a ranar 23 ga Oktoba, 2024.

ADVERTISEMENT
  • Kimanin ‘Ya’yan Jam’iyyar APC 1,000 Sun Sauya Sheƙa Zuwa NNPP A Kano

Sanarwar ta ƙara da cewa, babbar Alƙalin jihar, Mai Shari’a Kulu Aliyu, wacce Mai Shari’a Mukhtar Yusha’u ya wakilta ta rantsar da Shugaban Hukumar Zaɓen.

zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Har ila yau, Gwamna Lawal ya sanar da mambobin majalisar zartarwar jihar yayin zamanta cewa halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 79 da ya yi na da matuƙar amfani.

Ya bayyana fatan hakan zai haifar da sakamako mai kyau a ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar al’ummar Zamfara.

Gwamnan ya ce, ya sanya hannu kan gyaran dokar zaɓe ta jihar Zamfara makwannin da suka gabata gabanin zaɓen ƙananan hukumomin da ke tafe.

Ya ce, “A bisa hukuncin da Kotun Ƙoli ta yanke a kwanan baya game da zaben ƙananan hukumomi, muna buƙatar mu gudanar da zabe a ƙananan hukumomin mu cikin aminci.

“A bisa ga rattaba hannu kan dokar da aka yi wa kwaskwarima, hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar za ta sanar da jadawalin zaben da wuri-wuri domin mu samu zababbun shugabannin ƙananan hukumomi a Jihar Zamfara.

 

“Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Zamfara (ZASIEC) za ta fito da tsare-tsare kan zaɓen, kuma ana sa ran dukkanmu za mu ba da goyon baya da haɗin kan da ya dace domin samun nasarar aikin.”

Bugu da ƙari, a yayin taron majalisar, Gwamna Lawal ya umurci Sakataren gwamnatin jiha da ya haɗa hannu da mataimakin gwamnan domin gaggauta shirya bikin ƙaddamar da Hukumar Bunƙasa Zuba Jari ta Jihar Zamfara (ZIPA) domin ta yi aiki yadda ya kamata.

zamfarazamfara

Gwamnan ya kuma sanar da majalisar cewa jihar a shirye take ta fara aikin rabon kuɗi na ‘NG-Cares’.

“Aikin zai ttallafa wa marasa galihu, matasa marasa aikin yi da mata a faɗin ƙananan hukumomi 14 na jihar. Za a kashe jimillar kuɗi kusan Naira Biliyan 4.9.

“Masu cin gajiyar wannan shiri za su kasance mutane 5000 na matalauta da marasa galihu; ɗaukar matasa da mata marasa aikin yi 6000; tallafin inganta rayuwa rayuwa ga matasa da mata 8000.

“Dole ne mu yi adalci da nuna jagoranci nagari ga dukkan al’ummar jiharmu,” in ji shi

zamfara
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
zamfara
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Mutane Kalilan Ne Suka Sace Dukiyar Nijeriya Ta Hanyar Tallafin Mai – Tinubu 

Ban Ji Dadin Abin Da Libya Ta Yi Wa Super Eagles Ba - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.