• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Yi Kira A Kara Yawan Sojoji A Jihar Don Yaki Da ‘Yan Bindiga

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnan Zamfara Ya Yi Kira A Kara Yawan Sojoji A Jihar Don Yaki Da ‘Yan Bindiga
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya yi kira da aka yawan sojojin da aike jihar, domin magance ayyukan ‘yan bindiga.

Gwamnan ya ziyarci Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, a Hedikwatar tsaro da ke Abuja.

  • Mutane 11 Sun Rasu, 30 Sun Jikkata A Rikicin Kabilanci A Filato – Gwamnati
  • HOTUNA: Yadda Jami’an Tsaro Suka Lalata Haramtacciyar Matatar Danyen Mai A Ribas

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa Gwamnan ya gana da Babban Hafsan tsaron ne domin tattauna batun matsalar tsaro a Jihar Zamfara.

A yayin taron, Gwamna Lawal ya bayyana damuwarsa kan yadda ake ci gaba da kai hare-hare a wasu sassan Jihar Zamfara.

Ya kuma yi kira ga Babban Hafsan tsaron ƙasar da ya tura ƙarin sojoji da makaman da suka dace zuwa jihar.

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

“A yau na zo nan ne domin tattaunawa kan matsalar rashin tsaro da ta addabi Jihar Zamfara. Na zo nan a ‘yan watannin da suka gabata saboda wannan batun.

“A ’yan kwanakin nan an sha fama da matsalar hare-haren ’yan bindiga a wasu yankunan jihar.

“A cikin makon nan an kai wani hari a Ƙaramar Hukumar Tsafe, wanda ya yi sanadin asarar rayuka, ciki har da Jami’in Rundunar Kare Jama’a “Askarawan Zamfara” (CPG), sannan wasu ’yan bindiga sun Æ™one motocin sojoji da suka haÉ—a da na jami’an CPG.

“Muna fama da ƙarancin sojoji a Zamfara saboda an sake tura wasu jami’an yankin Arewa maso Gabas.

“Manoma ba sa iya noma gonakinsu, kuma hare-haren da ake ci gaba da kaiwa ya janyo asarar rayuka da dama.

“Ina so in yi amfani da wannan dama wajen kira gare ku da ku haɗa ƙarfi da ƙarfe domin tura ƙarin sojoji zuwa Zamfara, irin wannan mataki na da matuƙar muhimmanci wajen yaƙi da matsalar rashin tsaro da kuma dawo da zaman lafiya a jihar.

“Tsarin jami’an tsaro babu shakka zai kwantar wa jama’a hankali tare da karya gwiwar masu aikata laifuka daga aikata munanan ayyukansu.

Da yake mayar da martani, Babban Hafsan tsaron ƙasa, Janar Christopher Gwabin Musa, ya yaba da ƙoƙarin Gwamna Lawal na yaƙi da ’yan bindiga a Zamfara.

Ya ce: “Ina godiya ga Æ™oÆ™arin da ka ke yi na yaÆ™ar rashin tsaro. Muna shirin daidaita al’amura a Zamfara kamar yadda muka yi a Maiduguri.

“Muna tattaunawa da dukkanin Kwamandoji da masu ruwa da tsaki don magance matsalar hare-haren, wanda ke matuÆ™ar sanya É“acin rai,” in ji Janar Musa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SojojiZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 11 Sun Rasu, 30 Sun Jikkata A Rikicin Kabilanci A Filato – Gwamnati

Next Post

Muna Sane Nijeriya Ta Tsare ÆŠan Kasarmu Ma’aikacin Binance – Amurka

Related

Za Mu RiÆ™e Wa Minista Tijjani MuÆ™aminsa Bayan HamÉ“arar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

3 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

4 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

5 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

6 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

6 hours ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

6 hours ago
Next Post
Muna Sane Nijeriya Ta Tsare ÆŠan Kasarmu Ma’aikacin Binance – Amurka

Muna Sane Nijeriya Ta Tsare ÆŠan Kasarmu Ma'aikacin Binance - Amurka

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu RiÆ™e Wa Minista Tijjani MuÆ™aminsa Bayan HamÉ“arar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.