Ministan kwadago Chris Ngige ya ce nan ba da jimawa ba gwamnatin tarayya za ta ayyana arin albashi ga ma’aikatan gwamnati domin rage radadin tashin farashin kayayyaki da ake fuskanta.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin da yake magana da manema labarai jim kadan bayan wata ganawar sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadarsa da ke Villa.
Ya ce kwamiti kan albashi da shugaban kasar ya kafa na sake duba batun albashin ma’aikata, kuma ana sa ran zai zo da bukatar karin albashin a shekara mai zuwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp