• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Ta Fara Binciken Ministar Jin ƙai Kan Umarnin Zuba Miliyan N585 A Asusun Ma’aikaciya – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Yajin aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon ƙorafe-ƙorafe da rahotannin zargin da ake yi wa Ministar Harkokin Agaji da Jinƙai, Dakta Betta Edu, Gwamnatin Tarayya ta fara binciken yadda aka zuba naira miliyan N585.2 a asusun ajiyar wata ma’aikaciyar gwamnati, bisa umarnin ita ministar.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana haka a ranar Lahadi cikin wata sanarwa ga manema labarai.

  • Matatar Ɗangote Ta Karɓi Jirgi Na Biyar Na Ɗanyen Mai
  • Tinubu Ya Bada Umarnin Binciken Ma’aikatar Jin Kai Kan Zargin Karkatar Da Miliyan N585

Ita dai Minista Betta Edu, ta na ci gaba da shan ragargaza daga ko’ina a faɗin ƙasar nan bayan an fallasa yadda ta bada umarnin a zuba zunzurutun kuɗi har naira miliyan N585.2 a cikin asusun banki na wata ma’aikaciyar gwamnati, wadda ita ce akawu mai kula da Kuɗaɗen Tallafin Marasa Galihu a ma’aikatar.

Dakta Edu ta fitar da wasiƙar bada umarnin zuba wa ma’aikaciyar kuɗin ne ga Akanta Janar na Tarayya a cikin Disamba, 2023, inda ta rubuta cewa a zuba kuɗin cikin asusun, duk da cewa yin hakan ya karya doka.

Duk da cewa Akanta Janar ya ce mata yin hakan karya doka ne, amma ya amince an biya kuɗin cikin aljihun asusun ma’aikaciyar, wanda ministar ta ce a zuba mata kuɗin.

Labarai Masu Nasaba

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Wannan ne ya jawo ce-ce-ku-ce da nuna damuwar da har Gwamnatin Tarayya ta gaggauta fara bincike.

Sai dai ita kuma Edu ta ce ba ta aikata wani laifi da ya saɓa wa doka ba, duk kuwa da cewa akwai tambayoyin da ma’aikatar ta ya kamata ta amsa, haka shi ma ofishin Akanta Janar ɗin akwai tambayoyin da ya kamata ya amsa domin warware zare da abawa.

Cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi, Idris ya ce yanzu haka gwamnati ta fara bincike, sannan kuma ta gamsu da yadda ‘yan Nijeriya su ka nuna damuwarsu dangane da wannan zargi da ake yi wa ita ministar.

Ya ci gaba da cewa, Gwamnatin Tarayya, a ƙarƙashin shugabancin Bola Tinubu, ba ta gudanar da ayyukan ta cikin ƙumbiya-ƙumbiya.

Ya ce gwamnatin za ta tura kuɗaɗe a inda ya dace kai-tsaye, domin ayyukan biyan buƙatun ‘yan Nijeriya.

Haka nan kuma Idris ya yi kira tare da bada shawara ga jama’a da cewa a maida hankali wajen samun sahihan bayanai daga Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai da ya ke jagoranta.

Hakan a cewar sanarwar sa, ya na da nasaba da ganin yadda ake ta yaɗa labarai da bayanai marasa tushe balle makama da su ka shafi Gwamnatin Tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlmundahanaEFCCMa'aikatar Jinƙai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Kasuwanci: Kasar Sin Tana Da Kyawawan Sharuddan Jawo Jarin Waje

Next Post

Equatorial Guinea Za Ta Daukaka Huldarta Da Sin Zuwa Wani Sabon Matsayi, In Ji Shugaban Kasar

Related

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

8 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

9 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

9 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

10 hours ago
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue
Labarai

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

11 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

13 hours ago
Next Post
Equatorial Guinea

Equatorial Guinea Za Ta Daukaka Huldarta Da Sin Zuwa Wani Sabon Matsayi, In Ji Shugaban Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.