• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Za Ta Dawo Da Sayar Wa Dangote Ɗanyen Mai Da Farashin Naira

by Khalid Idris Doya
6 months ago
in Tattalin Arziki
0
Gwamnati Za Ta Dawo Da Sayar Wa Dangote Ɗanyen Mai Da Farashin Naira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da akwai yiyuwar shirin gwamnatin tarayya na sayar da danyen mai a kan naira zai ci gaba, inda majiyoyi suka tsegunta wannan batun a ranar Litinin tare da cewa dukkanin bangarorin da abun ya shafa za su koma teburin tattaunawa kwanan nan domin ganin sake dawo da harkar danyen mai a kan farashin Naira. 

Hada-hadar cinikayyar danyen mai a kan naira na wata shida tsakanin gwamnatin tarayya, kamfanin kula da albarkatun mai da matatar man dangote ya kawo karshen ne dai a ranar 31 ga watan Maris din 2023.

  • Sarki Sanusi Ya Yabawa Gwamna Yusuf Kan Manufofin Haɓaka Jama’ar Kano
  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF

Tuni dai matatar man dangote ta dakatar da sayar da man fetur a kan naira sai dala, sakamakon cewa ita da dala take sayen danyen man.

Wannan na zuwa ne a yayin da wani rahoto da S&P Global ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana cewa matatar dangote na sarrafa kusan ganga 400,000 a kowace rana ta danyen mai a shekarar 2025, inda kusan kashi 35 cikin 100 na wannan danyen mai din kamfanin na sayowa ne daga kasashen waje.

Hakan na nufin kamfanin na shigo da gangar danyen mai kusan ganga 140,000 a kowace rana da jimillar ganga miliyan 12.6 a cikin watanni uku.

Labarai Masu Nasaba

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan sayar da danyen mai da naira, wani babban jami’in gwamnati wanda ke da masaniya sosai kan lamarin da ke aiki da kwamitin da aka kafa don shirin ya bayyana cewa gwamnati ba wai ta dakatar da tsarin bane gaba daya.

“Shirin cinikayyar danyen mai a kan naira zai ci gaba saboda na gano cewa tsarin ya yi tasiri sosai ba kawai a kan farashin mai ba, har ma da kyautata ci gaban tattalin arziki.

“Bugu da kari, kwamitin yana jiran hukumar da ke kula da harkokin man fetur ta Nijeriya ta gabatar da rahoton aikin da aka ba ta dangane da wannan manufar. Da zarar an yi haka, abu na gaba shi ne a duba abun da za a yi na gaba kan wannan batun hada-hadar mai da kudin naira,” cewar majiyar wanda ya nemi a dakaye sunansa.

Idan za a tuna dai, a ranar 1 ga watan Oktoban 2024 ne gwamnati ta fara sayar da danyen mai a kan naira ga matatar man dangote domin inganta samar da man fetur, lamarin ya kai ga taimaka wa kasar nan da samun rarar miliyoyi na dala da take narkawa wajen sayo danyen mai daga kasashen waje, kuma shirin ya taimaka sosai wajen samun ragi kan farashin fetur.

A baya-bayan nan, kakakin kamfanin NNPC, Olufemi Shoneye yayin da ke fashin karin haske kan batun karewar hada-hadar cinikin, inda ya ce, “Bari na fayyace wannan lamarin, daman an kulla yarjejeniya ce na watanni shida, ya danganci wadatar danyen mai, kuma zai kare ne a karshen watan Maris na 2025.

“Tattaunawa na ci gaba da gudanar kan yadda za a kulla sabuwar yarjejeniya.

“A karkashin wannan yarjejeniyar, NNPC ya samar da danyen mai sama da ganga miliyan 48 ga matatar dangote tun watan Oktoban 2024.

“A takaice, NNPC ya samar da danyen mai ganga miliyan 84 ga matatar tun lokacin da ta fara aiki a shekarar 2023.

“NNPC ya himma wajen samar da danyen mai ga matatun mai na cikin gida a bisa tsarin yarjejeniya da sharuddan da aka cimma,” ya shaida.

Kazalika, rahoton S&P ya nuna cewa matatar mai ta dangote ta sayo danyen mai na farko ne daga kasar Burazil da Ekuatorial Guinea.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangoteNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhanin Rasuwar Shaikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi 

Next Post

Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

Related

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

2 days ago
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

2 days ago
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

1 week ago
Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar

1 week ago
Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto
Tattalin Arziki

Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto

1 week ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

3 weeks ago
Next Post
Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.