• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Za Ta Dawo Da Sayar Wa Dangote Ɗanyen Mai Da Farashin Naira

by Khalid Idris Doya
1 month ago
in Tattalin Arziki
0
Gwamnati Za Ta Dawo Da Sayar Wa Dangote Ɗanyen Mai Da Farashin Naira
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da akwai yiyuwar shirin gwamnatin tarayya na sayar da danyen mai a kan naira zai ci gaba, inda majiyoyi suka tsegunta wannan batun a ranar Litinin tare da cewa dukkanin bangarorin da abun ya shafa za su koma teburin tattaunawa kwanan nan domin ganin sake dawo da harkar danyen mai a kan farashin Naira. 

Hada-hadar cinikayyar danyen mai a kan naira na wata shida tsakanin gwamnatin tarayya, kamfanin kula da albarkatun mai da matatar man dangote ya kawo karshen ne dai a ranar 31 ga watan Maris din 2023.

  • Sarki Sanusi Ya Yabawa Gwamna Yusuf Kan Manufofin Haɓaka Jama’ar Kano
  • Nijar Ta Fice Daga Rundunar Tsaro Ta Haɗin Kai MNJTF

Tuni dai matatar man dangote ta dakatar da sayar da man fetur a kan naira sai dala, sakamakon cewa ita da dala take sayen danyen man.

Wannan na zuwa ne a yayin da wani rahoto da S&P Global ya fitar a ranar Litinin, ya bayyana cewa matatar dangote na sarrafa kusan ganga 400,000 a kowace rana ta danyen mai a shekarar 2025, inda kusan kashi 35 cikin 100 na wannan danyen mai din kamfanin na sayowa ne daga kasashen waje.

Hakan na nufin kamfanin na shigo da gangar danyen mai kusan ganga 140,000 a kowace rana da jimillar ganga miliyan 12.6 a cikin watanni uku.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan sayar da danyen mai da naira, wani babban jami’in gwamnati wanda ke da masaniya sosai kan lamarin da ke aiki da kwamitin da aka kafa don shirin ya bayyana cewa gwamnati ba wai ta dakatar da tsarin bane gaba daya.

“Shirin cinikayyar danyen mai a kan naira zai ci gaba saboda na gano cewa tsarin ya yi tasiri sosai ba kawai a kan farashin mai ba, har ma da kyautata ci gaban tattalin arziki.

“Bugu da kari, kwamitin yana jiran hukumar da ke kula da harkokin man fetur ta Nijeriya ta gabatar da rahoton aikin da aka ba ta dangane da wannan manufar. Da zarar an yi haka, abu na gaba shi ne a duba abun da za a yi na gaba kan wannan batun hada-hadar mai da kudin naira,” cewar majiyar wanda ya nemi a dakaye sunansa.

Idan za a tuna dai, a ranar 1 ga watan Oktoban 2024 ne gwamnati ta fara sayar da danyen mai a kan naira ga matatar man dangote domin inganta samar da man fetur, lamarin ya kai ga taimaka wa kasar nan da samun rarar miliyoyi na dala da take narkawa wajen sayo danyen mai daga kasashen waje, kuma shirin ya taimaka sosai wajen samun ragi kan farashin fetur.

A baya-bayan nan, kakakin kamfanin NNPC, Olufemi Shoneye yayin da ke fashin karin haske kan batun karewar hada-hadar cinikin, inda ya ce, “Bari na fayyace wannan lamarin, daman an kulla yarjejeniya ce na watanni shida, ya danganci wadatar danyen mai, kuma zai kare ne a karshen watan Maris na 2025.

“Tattaunawa na ci gaba da gudanar kan yadda za a kulla sabuwar yarjejeniya.

“A karkashin wannan yarjejeniyar, NNPC ya samar da danyen mai sama da ganga miliyan 48 ga matatar dangote tun watan Oktoban 2024.

“A takaice, NNPC ya samar da danyen mai ganga miliyan 84 ga matatar tun lokacin da ta fara aiki a shekarar 2023.

“NNPC ya himma wajen samar da danyen mai ga matatun mai na cikin gida a bisa tsarin yarjejeniya da sharuddan da aka cimma,” ya shaida.

Kazalika, rahoton S&P ya nuna cewa matatar mai ta dangote ta sayo danyen mai na farko ne daga kasar Burazil da Ekuatorial Guinea.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangoteNaira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhanin Rasuwar Shaikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi 

Next Post

Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

Related

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

2 weeks ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

3 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

3 weeks ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

4 weeks ago
Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97
Tattalin Arziki

Bankin Zenith Ya Samu Ribar Naira Tiriliyan 3.97

4 weeks ago
Next Post
Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

Bankin Duniya Zai Amince Da Buƙatar Nijeriya Na Amsar Rancen Dala Miliyan 632

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.