• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta caccaki gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu saboda rashin dubarun shugabanci, inda ta ce gwamnatin APC ta kara ingiza ‘yan Nijeriya da dama cikin bakin talauci.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba shi ya bay-yana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja. Ya ce dabi’u da manufofin jam’iyyar APC na yaudara tun bayan ka-fuwarta a shekarar 2014 da kuma hawan mulkita a 2015, ba wai kawai ta sanya Nijeriya ta zama cibiyar talauci a duniya ba, har ma ta jefa ‘yan Nijeriya cikin mawuyacin hali ta hanyar manufofinta mara su kyau.

  • Sin Ta Mikawa Gwamnatin Sudan Kashin Farko Na Tallafin Jin Kai 
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Amsa Tambaya Game Da Taron Ministocin Muhalli Da Yanayi Na G20

A cewar Ologunagba, jawabin shugaban kasa na ranar Litini, kokari ne kawai na kawar da hankalin ’yan Nijeriya daga halin kuncin da suke ciki da kuma yawan alkawuran da gwamnatin Tinubu ta yi.

Ya bayyana cewa jam’iyyar APC ta jajirce ne kawai ga muradun kasashen waje wanda suke bisa turbar kuskure da ba za su haifar wa kasar nan da mai ido ba.

Ya kara da cewa jawabin shugaban ba shi da wani tanadi na tsaron yankunan bakin teku da kuma jigilar ruwa a yankunan kogin, wanda ya kasance tubulin tat-talin arzikin Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Ya ce APC ta hau mulki ne ta hanyar farfaganda kuma ba ta cika alkawuran da ta yi wa ‘yan Nijeriya ba har yau.

“A yammacin Litinin, Sanata Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC ya kashe wa ‘yan Nijeriya fatan da suke da shi, musamman magoya bayansa da ke cikin rudani a yanzu, tare da gabatar da jawabinsa na kare kai daga munanan tsare-tsare da kuma manufofinsa mara amfani ga kasar nan. Jam’iyyar PDP koka kan yadda za a samu irin wannan rashin adalci wanda ya kara nuna rashin dabarar shugabanci da mayar da hannun agogo baya a kasar nan.

“Jam’iyyar PDP ta yi matukar kaduwa da wannan jawabi na shugaban kasa na alkawuran karya da ya yi.

“Yan Nijeriya sun san cewa jam’iyyar APC tare da Tinubu ba za su iya cika wadan-nan alkawuran da suka dauka ba, sun mayar da al’ummarmu wata cibiyar talauci ta duniya, inda sama da ‘yan kasa miliyan 100 ba za su iya cin abincin yau da kul-lum ba sakamakon hauhawar farashin kayayyakin masarufi. Tabbas babu wani abu sabo daga cikin kalamun Shugaba Tinubu, alkawaruka ne kawai a takarda amma ba za a iya zantar da su ba.

“Jawabin da Shugaban kasa ya yi babu wasu hanyoyi na kawo mafita sai dai ‘yan Nijeriya ci gaba da shan wahala da tsadar rayuwa sakamakon rashin sanin maka-man aikin gwamnatin APC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Yi Kokarin Magance Tushen Matsalar Karancin Abinci

Next Post

‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 day ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 days ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 week ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

1 week ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
Next Post
‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara

'Yansanda Sun Dakile Harin 'Yan Bindiga A Masallacin Juma'a A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.