• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta caccaki gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu saboda rashin dubarun shugabanci, inda ta ce gwamnatin APC ta kara ingiza ‘yan Nijeriya da dama cikin bakin talauci.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba shi ya bay-yana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja. Ya ce dabi’u da manufofin jam’iyyar APC na yaudara tun bayan ka-fuwarta a shekarar 2014 da kuma hawan mulkita a 2015, ba wai kawai ta sanya Nijeriya ta zama cibiyar talauci a duniya ba, har ma ta jefa ‘yan Nijeriya cikin mawuyacin hali ta hanyar manufofinta mara su kyau.

  • Sin Ta Mikawa Gwamnatin Sudan Kashin Farko Na Tallafin Jin Kai 
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Amsa Tambaya Game Da Taron Ministocin Muhalli Da Yanayi Na G20

A cewar Ologunagba, jawabin shugaban kasa na ranar Litini, kokari ne kawai na kawar da hankalin ’yan Nijeriya daga halin kuncin da suke ciki da kuma yawan alkawuran da gwamnatin Tinubu ta yi.

Ya bayyana cewa jam’iyyar APC ta jajirce ne kawai ga muradun kasashen waje wanda suke bisa turbar kuskure da ba za su haifar wa kasar nan da mai ido ba.

Ya kara da cewa jawabin shugaban ba shi da wani tanadi na tsaron yankunan bakin teku da kuma jigilar ruwa a yankunan kogin, wanda ya kasance tubulin tat-talin arzikin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Ya ce APC ta hau mulki ne ta hanyar farfaganda kuma ba ta cika alkawuran da ta yi wa ‘yan Nijeriya ba har yau.

“A yammacin Litinin, Sanata Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC ya kashe wa ‘yan Nijeriya fatan da suke da shi, musamman magoya bayansa da ke cikin rudani a yanzu, tare da gabatar da jawabinsa na kare kai daga munanan tsare-tsare da kuma manufofinsa mara amfani ga kasar nan. Jam’iyyar PDP koka kan yadda za a samu irin wannan rashin adalci wanda ya kara nuna rashin dabarar shugabanci da mayar da hannun agogo baya a kasar nan.

“Jam’iyyar PDP ta yi matukar kaduwa da wannan jawabi na shugaban kasa na alkawuran karya da ya yi.

“Yan Nijeriya sun san cewa jam’iyyar APC tare da Tinubu ba za su iya cika wadan-nan alkawuran da suka dauka ba, sun mayar da al’ummarmu wata cibiyar talauci ta duniya, inda sama da ‘yan kasa miliyan 100 ba za su iya cin abincin yau da kul-lum ba sakamakon hauhawar farashin kayayyakin masarufi. Tabbas babu wani abu sabo daga cikin kalamun Shugaba Tinubu, alkawaruka ne kawai a takarda amma ba za a iya zantar da su ba.

“Jawabin da Shugaban kasa ya yi babu wasu hanyoyi na kawo mafita sai dai ‘yan Nijeriya ci gaba da shan wahala da tsadar rayuwa sakamakon rashin sanin maka-man aikin gwamnatin APC.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara

'Yansanda Sun Dakile Harin 'Yan Bindiga A Masallacin Juma'a A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.