ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta caccaki gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu saboda rashin dubarun shugabanci, inda ta ce gwamnatin APC ta kara ingiza ‘yan Nijeriya da dama cikin bakin talauci.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba shi ya bay-yana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja. Ya ce dabi’u da manufofin jam’iyyar APC na yaudara tun bayan ka-fuwarta a shekarar 2014 da kuma hawan mulkita a 2015, ba wai kawai ta sanya Nijeriya ta zama cibiyar talauci a duniya ba, har ma ta jefa ‘yan Nijeriya cikin mawuyacin hali ta hanyar manufofinta mara su kyau.

  • Sin Ta Mikawa Gwamnatin Sudan Kashin Farko Na Tallafin Jin Kai 
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Amsa Tambaya Game Da Taron Ministocin Muhalli Da Yanayi Na G20

A cewar Ologunagba, jawabin shugaban kasa na ranar Litini, kokari ne kawai na kawar da hankalin ’yan Nijeriya daga halin kuncin da suke ciki da kuma yawan alkawuran da gwamnatin Tinubu ta yi.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa jam’iyyar APC ta jajirce ne kawai ga muradun kasashen waje wanda suke bisa turbar kuskure da ba za su haifar wa kasar nan da mai ido ba.

Ya kara da cewa jawabin shugaban ba shi da wani tanadi na tsaron yankunan bakin teku da kuma jigilar ruwa a yankunan kogin, wanda ya kasance tubulin tat-talin arzikin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Ya ce APC ta hau mulki ne ta hanyar farfaganda kuma ba ta cika alkawuran da ta yi wa ‘yan Nijeriya ba har yau.

“A yammacin Litinin, Sanata Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC ya kashe wa ‘yan Nijeriya fatan da suke da shi, musamman magoya bayansa da ke cikin rudani a yanzu, tare da gabatar da jawabinsa na kare kai daga munanan tsare-tsare da kuma manufofinsa mara amfani ga kasar nan. Jam’iyyar PDP koka kan yadda za a samu irin wannan rashin adalci wanda ya kara nuna rashin dabarar shugabanci da mayar da hannun agogo baya a kasar nan.

“Jam’iyyar PDP ta yi matukar kaduwa da wannan jawabi na shugaban kasa na alkawuran karya da ya yi.

“Yan Nijeriya sun san cewa jam’iyyar APC tare da Tinubu ba za su iya cika wadan-nan alkawuran da suka dauka ba, sun mayar da al’ummarmu wata cibiyar talauci ta duniya, inda sama da ‘yan kasa miliyan 100 ba za su iya cin abincin yau da kul-lum ba sakamakon hauhawar farashin kayayyakin masarufi. Tabbas babu wani abu sabo daga cikin kalamun Shugaba Tinubu, alkawaruka ne kawai a takarda amma ba za a iya zantar da su ba.

“Jawabin da Shugaban kasa ya yi babu wasu hanyoyi na kawo mafita sai dai ‘yan Nijeriya ci gaba da shan wahala da tsadar rayuwa sakamakon rashin sanin maka-man aikin gwamnatin APC.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara

'Yansanda Sun Dakile Harin 'Yan Bindiga A Masallacin Juma'a A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.