ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
PDP

Jam’iyyar PDP ta caccaki gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu saboda rashin dubarun shugabanci, inda ta ce gwamnatin APC ta kara ingiza ‘yan Nijeriya da dama cikin bakin talauci.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba shi ya bay-yana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja. Ya ce dabi’u da manufofin jam’iyyar APC na yaudara tun bayan ka-fuwarta a shekarar 2014 da kuma hawan mulkita a 2015, ba wai kawai ta sanya Nijeriya ta zama cibiyar talauci a duniya ba, har ma ta jefa ‘yan Nijeriya cikin mawuyacin hali ta hanyar manufofinta mara su kyau.

  • Sin Ta Mikawa Gwamnatin Sudan Kashin Farko Na Tallafin Jin Kai 
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Amsa Tambaya Game Da Taron Ministocin Muhalli Da Yanayi Na G20

A cewar Ologunagba, jawabin shugaban kasa na ranar Litini, kokari ne kawai na kawar da hankalin ’yan Nijeriya daga halin kuncin da suke ciki da kuma yawan alkawuran da gwamnatin Tinubu ta yi.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa jam’iyyar APC ta jajirce ne kawai ga muradun kasashen waje wanda suke bisa turbar kuskure da ba za su haifar wa kasar nan da mai ido ba.

Ya kara da cewa jawabin shugaban ba shi da wani tanadi na tsaron yankunan bakin teku da kuma jigilar ruwa a yankunan kogin, wanda ya kasance tubulin tat-talin arzikin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Ya ce APC ta hau mulki ne ta hanyar farfaganda kuma ba ta cika alkawuran da ta yi wa ‘yan Nijeriya ba har yau.

“A yammacin Litinin, Sanata Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC ya kashe wa ‘yan Nijeriya fatan da suke da shi, musamman magoya bayansa da ke cikin rudani a yanzu, tare da gabatar da jawabinsa na kare kai daga munanan tsare-tsare da kuma manufofinsa mara amfani ga kasar nan. Jam’iyyar PDP koka kan yadda za a samu irin wannan rashin adalci wanda ya kara nuna rashin dabarar shugabanci da mayar da hannun agogo baya a kasar nan.

“Jam’iyyar PDP ta yi matukar kaduwa da wannan jawabi na shugaban kasa na alkawuran karya da ya yi.

“Yan Nijeriya sun san cewa jam’iyyar APC tare da Tinubu ba za su iya cika wadan-nan alkawuran da suka dauka ba, sun mayar da al’ummarmu wata cibiyar talauci ta duniya, inda sama da ‘yan kasa miliyan 100 ba za su iya cin abincin yau da kul-lum ba sakamakon hauhawar farashin kayayyakin masarufi. Tabbas babu wani abu sabo daga cikin kalamun Shugaba Tinubu, alkawaruka ne kawai a takarda amma ba za a iya zantar da su ba.

“Jawabin da Shugaban kasa ya yi babu wasu hanyoyi na kawo mafita sai dai ‘yan Nijeriya ci gaba da shan wahala da tsadar rayuwa sakamakon rashin sanin maka-man aikin gwamnatin APC.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

PDP
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Masallacin Juma’a A Zamfara

'Yansanda Sun Dakile Harin 'Yan Bindiga A Masallacin Juma'a A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.