• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Gwamna Bala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Litinin da ta gabata ce, gwamnatin Jihar Bauchi ta tashi tsaye domin ganin ta tunkari matsalar yunwa da karancin abinci, inda ta kafa kwamitin saye da adana kayayyakin abinci domin fito da su a lokacin da suka fara wahalar samuwa domin shigar da su cikin jama’a.

 

Kwamitin wanda zai shiga lungu da sako na jihar wajen sayen kayan abinci daga hannun manoma a lokacin girbi domin yin goyayya da masu zuwa su saya daga jihar zuwa wasu jihohi da ma wasu kasashe.

  • Mata A Dage Da Karatu Yin Haka Taimakon Kanku Ne Da ‘Ya’yanku – Zainab Ahmad
  • Shaharrun Mutanen Da Suka Halarci Bikin Auren ‘Yar Kwankwaso

A cewar gwamnan jihar, Bala Muhammad a yayin rantsar da mambobin kwamitin, an yi wannan tsarin ne domin yaki da yunwa da fatara da kuma taimaka wa talakawan da suke jihar, uwa-uba da kuma daukan matakan shawo kan matsin rayuwa da ake fuskanta.

 

Labarai Masu Nasaba

Putin Ya Fita Daga Raina – Trump

Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

Ya ce, abun kunya ne kamar Jihar Bauchi da Allah ya huwace mata manoma da albarkatun noma a wayi gari a ce ana bukatar abinci, ya ce, sun nazarci cewa babbar matsalar kawai shi ne manoma na sayar da kayan abincin ga wasu da suke zuwa daga waje domin saye da fitar da su, don haka ba za su zura ido suna bari hakan na faruwa ba.

 

Sai dai, ya ce, ba za su hana manoma sayar da kayan amfaninsu ga kowa ba, illa za su yi hikima da dabarar yin gasa wajen saye domin taimaka wa al’umman jihar a lokacin da za a shiga neman abinci gadan-gadan.

 

Gwamnan ya sanar da ware naira biliyan uku ga kwamitin a matsayin kudin jari, ya kuma sanar da cewa, akwai damar za a iya kara wa kwamitin kudade domin ba su damar zuwa ko’ina su sayo kayan abinci a wajen manoma domin ajiyesu har zuwa lokacin da za a fito da su wajen taimaka wa jama’a.

 

Bala ya hori kwamitin za su yi amfani da hikima da dabarbarunsu domin kyautata tattalin arziki da kuma taimaka wa jama’a wajen rage yunwa da fatara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kaddamar Da Shirin Bidiyo Na CMG Mai Taken “Daga Great Wall zuwa Machu Picchu”

Next Post

Karancin Kudin Shiga Ya Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya

Related

Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka
Labarai

Putin Ya Fita Daga Raina – Trump

2 hours ago
Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN
Labarai

Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

3 hours ago
Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?
Ra'ayi Riga

Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

7 hours ago
Mutuwar Malamin Jami’a A Otel: Jami’ar Kogi Za Ta Gudanar Da Bincike
Manyan Labarai

Mutuwar Malamin Jami’a A Otel: Jami’ar Kogi Za Ta Gudanar Da Bincike

7 hours ago
‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna
Labarai

‘Yansanda Sun Hana Gudanar Da Taron Tunawa Da Ranar Haihuwar Obi A Kaduna

11 hours ago
sallah
Labarai

Yadda Hauhawar Farashin Kayan Abinci Ya Ragu A Nijeriya

12 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Karancin Kudin Shiga Ya Jefa 'Yan Nijeriya Miliyan 14 Cikin Kangin Talauci – Bankin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

July 19, 2025
An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

July 19, 2025
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

Putin Ya Fita Daga Raina – Trump

July 19, 2025
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

July 19, 2025
Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

July 19, 2025
Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

July 19, 2025
Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

July 19, 2025
Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana

Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana

July 19, 2025
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

July 19, 2025
Xi Da Takwaransa Na Mauritania Ghazouani Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

Xi Da Takwaransa Na Mauritania Ghazouani Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

July 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.