• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan baya, yayin da firaministan kasar Girka Kyriakos Mitsotakis, ke ziyara a kasar Birtaniya, ya yi shirin ganawa da takwaransa na Birtaniya, Rishi Sunak, gami da tattaunawa tare da shi kan batun mayar wa kasar Girka da mutum-mutumin wurin ibada na Parthenon da gidan adana kayayyakin tarihi na kasar Birtaniya wato the British Museum ya mallaka. Sai dai, bayan da Mista Sunak ya ji yadda za a ambaci batun mayar da kayayyakin tarihi, nan take ya soke shirin ganawar, lamarin da ya fusata bangaren Girka sosai, har ma wasu kafofin watsa labaru na kasar Birtaniya su ma sun ce soke ganawar da Mista Sunak ya yi mataki maras ladabi ne. Sai dai a ganina, maimakon bayyana batun nan a matsayin wani mataki na maras ladabi da da’a, gara a ce Mista Sunak yana damuwa da jin tsoro. Kamar dai yadda Mitsotakis ya bayyana bayan abkuwar lamarin, inda ya ce “Duk wani dake da kwarin gwiwa kan gaskiyar matsayinsa, ba zai ji tsoron muhawara tare da saura fuska da fuska ba.” A zahiri dai, yadda Mista Sunak ya magance muhawara ya nuna ra’ayin gwamnatin kasar Birtaniya na damuwa kan yadda take mallakar kayayyakin tarihi na sauran kasashe daban daban.

Tabbas kasar Birtaniya za ta damu, saboda ta samu dimbin kayayyakin tarihi masu daraja da ake ajiyarsu cikin gidan adana kayayyakin tarihi na the British Museum ne, ta hanyar mulkin mallaka da wasoso a sauran kasashe. Kana a cikin kayayyakin da aka kwata, har da wasu kayayyakin tagulla fiye da 900 na kasar Najeriya. An bayyana sarai a shafin yanar gizo ko Internet na British Museum cewa sojojin kasar Birtaniya ne suka kwaci wadannan kayayyakin tagulla daga kasar Najeriya, lokacin da suka kai hari ga daular Benin a shekarar 1897. Saboda haka, cikin shekarun da suka gabata, kasashe da yawa da suka hada Girka, da Najeriya, da Habasha, da Masar, wadanda yawancinsu kasashe ne masu tasowa, sun yi ta kokarin matsawa gwamnatin kasar Birtaniya lamba, don ta mayar musu da kayayyakin tarihinsu.

  • Jami’ar EDF: Matakan Lardin Guangdong Na Sin Kan Magance Sauyin Yanayi Abin Koyi Ne
  • Shahararren Masanin Kasar Sin: Rasuwar Kissinger Ta Karfafa Gwiwar Bude Sabon Babi Ga Alakar Kasa Da Kasa

Sai dai, Birtaniya ba ta taba yarda da bukatar wadannan kasashe mai adalci ba, bisa dalilin wai dokarta ta hana a mayar da kayayyakin. A cewar kafofin watsa labaru na kasar Birtaniya, ainihin dalilin da ya sa kasar Birtaniya kin biyan bukatun wadannan kasashe, shi ne domin a ganinta, kasashen ba su da kwarewar da ake bukata a fannin kare kayayyakin tarihi. Dole ne a bar kayayyakin a hannun ’yan kasashen yammacin duniya, idan ana son kare su da nazari a kansu, saboda kasashen yamma cibiyar dan Adam ce ta kare al’adu da wayewar kai, wannan tunani ne na kasar Birtaniya, amma ko da gaske ne haka? A watan Agustan bana, wasu kayayyaki kimanin 2000 sun bace daga British Museum, inda har ma aka sayar da wasunsu ta shafin yanar gizo ko Internet, lamarin da ya nuna gazawar gwamnatin kasar Birtaniya a fannin kare kayayyakin tarihi.

Ko da yake ta kasa kare wadannan kayayyaki da kyau, amma duk da haka, gwamnatin kasar Birtaniya ta ci gaba da kin amincewa da mayar da su. Me ya sa take yin haka? A ganina, wasu mutanen Birtaniya na ci gaba da rike da tunanin “Kasancewar kasashen yamma cibiyar duiya”. Wato bayan da suka ga dimbin kayayyakin tarihi na kasashe daban daban da ake baje kolinsu cikin Museum din su, to, za su yi mafarki tamkar su ne suka gaji daukacin al’adun dan Adam, kana wai tarihi ya nuna cewa hanyar raya kasa ta kasashen yamma daidaitaciyar hanya ce daya tilo a duniya. Sa’an nan, lokacin da kasashe masu tasowa sun nemi a mayar musu da kayayyakinsu, mutanen Birtaniya za su ji tamkar ana neman farkar da su daga wani mafarki ne, amma fa ba su son farkewa. Saboda haka, sun fara magance tattaunawa, da damuwa a zuci, gami da rashin abin da ya kamata su yi.

Amma, tabbas ne za a farka, kome dadin mafarkin da ake yi. Wani yanayin da ake samu a duniyarmu shi ne, tasowar kasashe masu tasowa, da yadda aka fara samun wani tsari na kasancewar bangarori masu fada a ji da yawa a duniya. Kana a nasu bangare, kasashe masu tasowa ba za su taba daina kokarin neman dawo da kayayyakin tarihinsu ba. Saboda wadannan kayayyaki sun kunshi bayanan tarihin al’ummunsu. Dole ne a kare wadannan kayayyakin, da nazari a kansu yadda ake bukata, sa’an nan za a samu damar karfafa tunanin mutane na zama mambobin wata al’umma, da imani kan al’adun musamman nasu. Daga baya, za a iya daina kwaikwayon dabarun kasashen yamma, da kokarin nazari kan wata hanyar raya kasa, wadda ta dace da yanayin da kasar ke ciki, don neman raya kasa ta wata hanyar musamman da aka zaba da kai.

Labarai Masu Nasaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Idan an duba wani rahoton binciken sauraron ra’ayin jama’ar kasashe daban daban, da kafar watsa labarai ta CGTN na kasar Sin ya kaddamar, za a ga cewar, kashi 92.3% na dukkan mutanen da suka bayyana ra’ayoyinsu, sun yi kira ga gwamnatin kasar Birtaniya da ta sauke nauyin dake bisa wuyanta, sa’an nan ta mayar da martani ga bukatun kasashen masu tasowa, na komar da kayayyakin tarihi gidajensu. Saboda batun tasowar kasashe masu tasowa a bayyane yake, kana bukatarsu na da adalci. Shin kasar Birtaniya za ta iya ci gaba da magance muhawara, da kin daukar nauyi, har zuwa yaushe? (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasar BirtaniyaKayan tarihiYakin Duniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

Next Post

Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya – Minista

Related

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

24 minutes ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

1 hour ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

20 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

21 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

22 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

23 hours ago
Next Post
Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya – Minista

Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya - Minista

LABARAI MASU NASABA

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.