• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Birtaniya Na Damuwa Kan Yadda Ake Neman A Mayar Da Kayayyakin Tarihi Da Ta Mallaka

by CGTN Hausa
2 years ago
Birtaniya

A kwanan baya, yayin da firaministan kasar Girka Kyriakos Mitsotakis, ke ziyara a kasar Birtaniya, ya yi shirin ganawa da takwaransa na Birtaniya, Rishi Sunak, gami da tattaunawa tare da shi kan batun mayar wa kasar Girka da mutum-mutumin wurin ibada na Parthenon da gidan adana kayayyakin tarihi na kasar Birtaniya wato the British Museum ya mallaka. Sai dai, bayan da Mista Sunak ya ji yadda za a ambaci batun mayar da kayayyakin tarihi, nan take ya soke shirin ganawar, lamarin da ya fusata bangaren Girka sosai, har ma wasu kafofin watsa labaru na kasar Birtaniya su ma sun ce soke ganawar da Mista Sunak ya yi mataki maras ladabi ne. Sai dai a ganina, maimakon bayyana batun nan a matsayin wani mataki na maras ladabi da da’a, gara a ce Mista Sunak yana damuwa da jin tsoro. Kamar dai yadda Mitsotakis ya bayyana bayan abkuwar lamarin, inda ya ce “Duk wani dake da kwarin gwiwa kan gaskiyar matsayinsa, ba zai ji tsoron muhawara tare da saura fuska da fuska ba.” A zahiri dai, yadda Mista Sunak ya magance muhawara ya nuna ra’ayin gwamnatin kasar Birtaniya na damuwa kan yadda take mallakar kayayyakin tarihi na sauran kasashe daban daban.

Tabbas kasar Birtaniya za ta damu, saboda ta samu dimbin kayayyakin tarihi masu daraja da ake ajiyarsu cikin gidan adana kayayyakin tarihi na the British Museum ne, ta hanyar mulkin mallaka da wasoso a sauran kasashe. Kana a cikin kayayyakin da aka kwata, har da wasu kayayyakin tagulla fiye da 900 na kasar Najeriya. An bayyana sarai a shafin yanar gizo ko Internet na British Museum cewa sojojin kasar Birtaniya ne suka kwaci wadannan kayayyakin tagulla daga kasar Najeriya, lokacin da suka kai hari ga daular Benin a shekarar 1897. Saboda haka, cikin shekarun da suka gabata, kasashe da yawa da suka hada Girka, da Najeriya, da Habasha, da Masar, wadanda yawancinsu kasashe ne masu tasowa, sun yi ta kokarin matsawa gwamnatin kasar Birtaniya lamba, don ta mayar musu da kayayyakin tarihinsu.

  • Jami’ar EDF: Matakan Lardin Guangdong Na Sin Kan Magance Sauyin Yanayi Abin Koyi Ne
  • Shahararren Masanin Kasar Sin: Rasuwar Kissinger Ta Karfafa Gwiwar Bude Sabon Babi Ga Alakar Kasa Da Kasa

Sai dai, Birtaniya ba ta taba yarda da bukatar wadannan kasashe mai adalci ba, bisa dalilin wai dokarta ta hana a mayar da kayayyakin. A cewar kafofin watsa labaru na kasar Birtaniya, ainihin dalilin da ya sa kasar Birtaniya kin biyan bukatun wadannan kasashe, shi ne domin a ganinta, kasashen ba su da kwarewar da ake bukata a fannin kare kayayyakin tarihi. Dole ne a bar kayayyakin a hannun ’yan kasashen yammacin duniya, idan ana son kare su da nazari a kansu, saboda kasashen yamma cibiyar dan Adam ce ta kare al’adu da wayewar kai, wannan tunani ne na kasar Birtaniya, amma ko da gaske ne haka? A watan Agustan bana, wasu kayayyaki kimanin 2000 sun bace daga British Museum, inda har ma aka sayar da wasunsu ta shafin yanar gizo ko Internet, lamarin da ya nuna gazawar gwamnatin kasar Birtaniya a fannin kare kayayyakin tarihi.

Ko da yake ta kasa kare wadannan kayayyaki da kyau, amma duk da haka, gwamnatin kasar Birtaniya ta ci gaba da kin amincewa da mayar da su. Me ya sa take yin haka? A ganina, wasu mutanen Birtaniya na ci gaba da rike da tunanin “Kasancewar kasashen yamma cibiyar duiya”. Wato bayan da suka ga dimbin kayayyakin tarihi na kasashe daban daban da ake baje kolinsu cikin Museum din su, to, za su yi mafarki tamkar su ne suka gaji daukacin al’adun dan Adam, kana wai tarihi ya nuna cewa hanyar raya kasa ta kasashen yamma daidaitaciyar hanya ce daya tilo a duniya. Sa’an nan, lokacin da kasashe masu tasowa sun nemi a mayar musu da kayayyakinsu, mutanen Birtaniya za su ji tamkar ana neman farkar da su daga wani mafarki ne, amma fa ba su son farkewa. Saboda haka, sun fara magance tattaunawa, da damuwa a zuci, gami da rashin abin da ya kamata su yi.

Amma, tabbas ne za a farka, kome dadin mafarkin da ake yi. Wani yanayin da ake samu a duniyarmu shi ne, tasowar kasashe masu tasowa, da yadda aka fara samun wani tsari na kasancewar bangarori masu fada a ji da yawa a duniya. Kana a nasu bangare, kasashe masu tasowa ba za su taba daina kokarin neman dawo da kayayyakin tarihinsu ba. Saboda wadannan kayayyaki sun kunshi bayanan tarihin al’ummunsu. Dole ne a kare wadannan kayayyakin, da nazari a kansu yadda ake bukata, sa’an nan za a samu damar karfafa tunanin mutane na zama mambobin wata al’umma, da imani kan al’adun musamman nasu. Daga baya, za a iya daina kwaikwayon dabarun kasashen yamma, da kokarin nazari kan wata hanyar raya kasa, wadda ta dace da yanayin da kasar ke ciki, don neman raya kasa ta wata hanyar musamman da aka zaba da kai.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

Idan an duba wani rahoton binciken sauraron ra’ayin jama’ar kasashe daban daban, da kafar watsa labarai ta CGTN na kasar Sin ya kaddamar, za a ga cewar, kashi 92.3% na dukkan mutanen da suka bayyana ra’ayoyinsu, sun yi kira ga gwamnatin kasar Birtaniya da ta sauke nauyin dake bisa wuyanta, sa’an nan ta mayar da martani ga bukatun kasashen masu tasowa, na komar da kayayyakin tarihi gidajensu. Saboda batun tasowar kasashe masu tasowa a bayyane yake, kana bukatarsu na da adalci. Shin kasar Birtaniya za ta iya ci gaba da magance muhawara, da kin daukar nauyi, har zuwa yaushe? (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal
Daga Birnin Sin

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025
Daga Birnin Sin

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
Next Post
Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya – Minista

Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya - Minista

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Birtaniya

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.