ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasafin 2024 Ya Bada Fifiko Ne Wajen Jaddada Ajandar Saisaita Nijeriya – Minista

by Sulaiman
3 years ago
Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Kasafin Kuɗi na shekarar 2024 ya nuna lallai an fara taka tsanin samun nasarorin ƙudirorin sake bunƙasa ƙasa a ƙarƙashin Ajandar Saisaita Nijeriya ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Asabar a Kaduna, yayin da ya ke jawabi a taron shekara wanda Cibiyar Faɗakar Da Jama’a ta Nijeriya (NIPR), reshen Jihar Kaduna, ta shirya.

  • SERAP  Ta Nemi Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar Gina Wa Shettima Gidan Naira Biliyan 15
  • Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana

Ya ce baki ɗayan kasafin 2024 an bijiro da shi ne bisa zurfafa nazarin manya da ƙananan ƙalubalen da ke fuskantar ƙasar nan, don haka ne aka tsara kasafin yadda zai fara da zaburar da hanyoyin bunƙasa ƙasa da kawo cigaba mai ɗorewa, inganta tattalin arziki da kuma wanzar da yalwar arziki a ƙasa baki ɗaya.

ADVERTISEMENT

Ya ce: “A cikin wannan satin ne Shugaba Bola Tinubu ya gabatar da Kasafin Kuɗi na 2024 na naira tiriliyan 27.5 ga Majalisar Tarayya, wanda shi ne kasafinsa na farko tun da ya kama mulkinsa. Kasafin kamar yadda ya gabatar da shi, bigire ne na fara taka tsanin tabbatar da cin nasarar Ajandar Saisaita Nijeriya, ta hanyar bada fifiko ga ƙudirorin gina ingantaccen tattalin arziki.

“Sannan kuma kasafin ya nuna yadda gwamnatin Tinubu ke taka-tsantsan da tsantseni wajen bada fifikon kashe kuɗaɗe a hanyoyin da su ka dace, domin ta hakan ake gina ginshiƙin tsarin tattalin arziki mai nisan zango.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

“Yayin da Kasafin Kuɗi na 2024 ya tafi hannun majalisa domin yin nazari da tsettsefe shi, mu na da kyakkyawan yaƙinin cewa kasafin zai kasance matakin farko na bin turbar saisaita Nijeriya, kawo cigaba da inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.”

Haka kuma Ministan ya ce kafin Shugaba Tinubu ya gabatar da kasafin, sai da ya yi ƙwarya-ƙwaryan kasafi, ya sa wa ƙudirori hannu sun zama doka, kuma ya kafa kwamitin shugaban ƙasa kan tsare-tsaren kuɗaɗe da tattalin arziki, kwamitin iskar gas (CNG), Shirin Bunƙasa Abinci, Shirin Tallafa wa Matsakaita da Ƙananan Masana’antu (MSME) da sauran fannoni masu muhimmanci wajen raya tattalin arziki.

Ya ce: “Muradin da ake so a cimma shi ne samar wa ɗan Nijeriya rayuwa cikin sauƙi, tare da gina tushen dawwamammen yalwar arziki.”

Ya ce tilas fa sai ‘yan Nijeriya sun bai wa wannan gwamnati uzirin cewa ta kama mulki a wani mawuyacin hali ne, amma kuma duk da haka shi Shugaban Ƙasa ya tarbi gaban kowane ƙalubalen da ake tunkara ko ya ke tunkaro ƙasar nan.

Minista
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Kotu Ta Umarci Dawo Da Motoci 50 Da Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Kwashe

Kotu Ta Umarci Dawo Da Motoci 50 Da Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Kwashe

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.