• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

by Sadiq
3 years ago
Ebonyi

Gwamnatin Jihar Ebonyi ta bai wa jami’an tsaro umarnin harbe duk wani bata garin da aka gani yana dauke da bindiga ko kuma wani makamin hallaka jama’a domin kawo karshen kashe-kashen da ake samu a jihar.

Kwamishinan yada labaran jihar, Uchenna Orji, ya ce wannan umarnin ya shafi rundunar tsaron sa kai ta jihar da aka yi wa suna Ebubeagu, wadda ita ma aka bai wa jami’anta wannan dama na hallaka wadannan tsageru.

  • ‘Yansanda Na Bincike Kan Cire Idon Wani Almajiri A Bauchi
  • Bikin Kirisimeti: Wanda Takardun Fasfonsa Ya Kare Zai Iya Dawo Wa Gida – Gwamnati

Rahotanni sun ce daukar wannan mataki ya biyo bayan tashin hankalin da aka gani samu a Litinin, inda wasu tsageru dauke da makamai da ake zargin magoya bayan haramcacciyar kungiyar IPOB ne, suka kutsa kai cikin birnin Abakaliki suna harbe-harbe da rana tsaka.

Lamarin da ya razana mutanen garin wadanda suka rufe shaguna da kasuwanni da kuma bankuna.

Bayanai sun ce ‘yan bindigar sun kai harin Abakaliki ne da zummar tabbatar da umarnin hana zirga-zirga na kwanaki biyar da shugaban wani sashe na kungiyar IPOB ya bayar.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Wannan hari ya yi sanadiyar hallaka wasu mutane tare da jikkata wasu da dama, duk da ya ke kwamishinan yada labaran jihar ya ce babu wanda ya rasa ransa sakamakon harbe-harben.

Orji, ya zargi maciya amanar jihar da yada labaran tilastawa mutane zaman gida da zummar razana su domin ganin ba su gudanar da harkokin su na yau da kullum ba.

Kwamishinan, ya ce Gwamna David Umahi, ya kuma bai wa jami’an tsaron da ke aiki a jihar, tare da rundunar Ebubeagu umarnin ci gaba da sintiri a Birnin Abakaliki da kuma wasu biranen jihar domin tabbatar da tsaro.

Idan dai ba a manta ba, Simon Ekpa, daya daga cikin shuganannin da ke fafutukar kafa kasar Biyafara, ya sanar da cewar za su kaddamar da shirin zaman gida na tilas na kwanaki biyar daga ranar 9 ga watan Disamba zuwa 14, a ci gaba da fafutukar ganin sun cimma muradunsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Next Post
Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

Sojoji Sun Fatattaki Boko Haram, Sun Ceto Mutane 86 Da Aka Sace A Borno

November 10, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.