• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

by Sadiq
3 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Ebonyi ta bai wa jami’an tsaro umarnin harbe duk wani bata garin da aka gani yana dauke da bindiga ko kuma wani makamin hallaka jama’a domin kawo karshen kashe-kashen da ake samu a jihar.

Kwamishinan yada labaran jihar, Uchenna Orji, ya ce wannan umarnin ya shafi rundunar tsaron sa kai ta jihar da aka yi wa suna Ebubeagu, wadda ita ma aka bai wa jami’anta wannan dama na hallaka wadannan tsageru.

  • ‘Yansanda Na Bincike Kan Cire Idon Wani Almajiri A Bauchi
  • Bikin Kirisimeti: Wanda Takardun Fasfonsa Ya Kare Zai Iya Dawo Wa Gida – Gwamnati

Rahotanni sun ce daukar wannan mataki ya biyo bayan tashin hankalin da aka gani samu a Litinin, inda wasu tsageru dauke da makamai da ake zargin magoya bayan haramcacciyar kungiyar IPOB ne, suka kutsa kai cikin birnin Abakaliki suna harbe-harbe da rana tsaka.

Lamarin da ya razana mutanen garin wadanda suka rufe shaguna da kasuwanni da kuma bankuna.

Bayanai sun ce ‘yan bindigar sun kai harin Abakaliki ne da zummar tabbatar da umarnin hana zirga-zirga na kwanaki biyar da shugaban wani sashe na kungiyar IPOB ya bayar.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

Wannan hari ya yi sanadiyar hallaka wasu mutane tare da jikkata wasu da dama, duk da ya ke kwamishinan yada labaran jihar ya ce babu wanda ya rasa ransa sakamakon harbe-harben.

Orji, ya zargi maciya amanar jihar da yada labaran tilastawa mutane zaman gida da zummar razana su domin ganin ba su gudanar da harkokin su na yau da kullum ba.

Kwamishinan, ya ce Gwamna David Umahi, ya kuma bai wa jami’an tsaron da ke aiki a jihar, tare da rundunar Ebubeagu umarnin ci gaba da sintiri a Birnin Abakaliki da kuma wasu biranen jihar domin tabbatar da tsaro.

Idan dai ba a manta ba, Simon Ekpa, daya daga cikin shuganannin da ke fafutukar kafa kasar Biyafara, ya sanar da cewar za su kaddamar da shirin zaman gida na tilas na kwanaki biyar daga ranar 9 ga watan Disamba zuwa 14, a ci gaba da fafutukar ganin sun cimma muradunsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BindigaEbonyiIPOBUmarni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Za Ku Taba Nadamar Zaben APC A Karkashin Mulkina Ba – Tinubu

Next Post

Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Related

Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Soke Ziyarar Kaduna, Zai Tafi Benuwe Saboda Rikice-Rikice

2 weeks ago
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

1 month ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

1 month ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

2 months ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

2 months ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

2 months ago
Next Post
Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.