• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa
0
Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Ebonyi ta bai wa jami’an tsaro umarnin harbe duk wani bata garin da aka gani yana dauke da bindiga ko kuma wani makamin hallaka jama’a domin kawo karshen kashe-kashen da ake samu a jihar.

Kwamishinan yada labaran jihar, Uchenna Orji, ya ce wannan umarnin ya shafi rundunar tsaron sa kai ta jihar da aka yi wa suna Ebubeagu, wadda ita ma aka bai wa jami’anta wannan dama na hallaka wadannan tsageru.

  • ‘Yansanda Na Bincike Kan Cire Idon Wani Almajiri A Bauchi
  • Bikin Kirisimeti: Wanda Takardun Fasfonsa Ya Kare Zai Iya Dawo Wa Gida – Gwamnati

Rahotanni sun ce daukar wannan mataki ya biyo bayan tashin hankalin da aka gani samu a Litinin, inda wasu tsageru dauke da makamai da ake zargin magoya bayan haramcacciyar kungiyar IPOB ne, suka kutsa kai cikin birnin Abakaliki suna harbe-harbe da rana tsaka.

Lamarin da ya razana mutanen garin wadanda suka rufe shaguna da kasuwanni da kuma bankuna.

Bayanai sun ce ‘yan bindigar sun kai harin Abakaliki ne da zummar tabbatar da umarnin hana zirga-zirga na kwanaki biyar da shugaban wani sashe na kungiyar IPOB ya bayar.

Labarai Masu Nasaba

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

Wannan hari ya yi sanadiyar hallaka wasu mutane tare da jikkata wasu da dama, duk da ya ke kwamishinan yada labaran jihar ya ce babu wanda ya rasa ransa sakamakon harbe-harben.

Orji, ya zargi maciya amanar jihar da yada labaran tilastawa mutane zaman gida da zummar razana su domin ganin ba su gudanar da harkokin su na yau da kullum ba.

Kwamishinan, ya ce Gwamna David Umahi, ya kuma bai wa jami’an tsaron da ke aiki a jihar, tare da rundunar Ebubeagu umarnin ci gaba da sintiri a Birnin Abakaliki da kuma wasu biranen jihar domin tabbatar da tsaro.

Idan dai ba a manta ba, Simon Ekpa, daya daga cikin shuganannin da ke fafutukar kafa kasar Biyafara, ya sanar da cewar za su kaddamar da shirin zaman gida na tilas na kwanaki biyar daga ranar 9 ga watan Disamba zuwa 14, a ci gaba da fafutukar ganin sun cimma muradunsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BindigaEbonyiIPOBUmarni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Za Ku Taba Nadamar Zaben APC A Karkashin Mulkina Ba – Tinubu

Next Post

Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Related

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

6 days ago
Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Barikin Sojoji A Borno, Bama-bamai Sun Fashe

2 weeks ago
Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita
Da ɗumi-ɗuminsa

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N835 Kan Kowace Lita

4 weeks ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

1 month ago
Ku Gafarce Ni, Na Yi Nadamar Tallata Tinubu Da Na Yi – Ɗanbilki Kwamanda
Da ɗumi-ɗuminsa

Ku Gafarce Ni, Na Yi Nadamar Tallata Tinubu Da Na Yi – Ɗanbilki Kwamanda

3 months ago
Umar Farouk Ibrahim (Sakataren Gwamnatin Kano)
Da ɗumi-ɗuminsa

Watanni 2 Da Sauke Baffa Bichi, An Nada Umar Farouk Mukamin Sakataren Gwamnatin Kano

3 months ago
Next Post
Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

Atiku Ya Taya Wike Murnar Cika Shekara 55 Duk Da Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.