ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya

by Sulaiman
2 years ago
Kaduna

Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Malam Uba Sani, ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta shirya tsaf don fara raba tallafi ga marasa karfi a jihar wadanda cire tallafin fetur ya jefa cikin mawuyacin hali. 

Gwamnatin jihar ta tattauna da shugabannin al’umma game da abun da ya fi cancanta gwamnatin ta yi akan Naira Biliyan biyu da gwamnatin tarayya ta fara bayarwa don tallafawa al’umma.

  • Gwamna Uba Sani Ya Sake Nadin Sabbin Mukamai A Jihar Kaduna 

Kwamitin gwamnatin karkashin jagorancin Mataimakiyar gwamnan, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe ne ya tattauna da shugabannin kungiyoyi masu zaman kansu, wakilan ‘yan kasuwa, wakilan ma’aikatan gwamnati, kungiyoyin Manoma da Malamai da sauransu.

ADVERTISEMENT

A sakamakon tattaunawar, kwamitocin sun cimma matsaya kan yadda za a kashe kudin, inda suka raba aikin zuwa gida Uku, kamar haka:

Na farko, za a siya buhunan shinkafa guda 40,000 wanda za a tabbatar mutum miliyan 1,050,000 marasa karfi sun amfana da wannan tallafin. Daga cikin biliyan biyun, za a kashe Naira biliyan N1,935,000,000 sannan ragowar Naira Miliyan N65,000,000 za a yi amfani da su wurin tallafawa marasa karfi don zuwa wurin da za a raba abincin.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Na biyu, za a hada kai da kungiyoyin sufuri kan rage kudin mota don taimakawa mutane wurin zirga-zirgarsu ta yau da kullum. Bayan wannan kuma, gwamnatin za ta siyo motocin sufuri na jihar Kaduna wanda za a rage kudinsu wasu kuma za a barsu shiga kyauta. Bugu da kari, gwamnatin za ta tabbatar ta samar da takin zamani don taimakawa manoma don bunkasa harkar Noma a jihar

Na Karshe, Gwamnan ya bayyana cewa, tuni ya fara tattauna da Sakataren Dindindin na ma’aikatar sufuri kuma zai gana da sabon Ministan sufuri kan yadda za a dawo da layin dogo da ke zirga-zirga acikin jihar wanda ke ta so wa daga Zaria zuwa cikin Kaduna sannan ya nufi Kafanchan.

Gwamnan ya kuma bukaci jama’a da su kara hakuri, ya jaddada aniyar gwamnatin jihar Kaduna wurin nemo mafita don inganta harkoki da rayuwar ‘yan jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Matar Aure Ta Kashe Dan Kishiyarta Mai Kwana 4 A Duniya A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.