ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya

by Sulaiman
3 years ago
Kaduna

Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Malam Uba Sani, ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta shirya tsaf don fara raba tallafi ga marasa karfi a jihar wadanda cire tallafin fetur ya jefa cikin mawuyacin hali. 

Gwamnatin jihar ta tattauna da shugabannin al’umma game da abun da ya fi cancanta gwamnatin ta yi akan Naira Biliyan biyu da gwamnatin tarayya ta fara bayarwa don tallafawa al’umma.

  • Gwamna Uba Sani Ya Sake Nadin Sabbin Mukamai A Jihar Kaduna 

Kwamitin gwamnatin karkashin jagorancin Mataimakiyar gwamnan, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe ne ya tattauna da shugabannin kungiyoyi masu zaman kansu, wakilan ‘yan kasuwa, wakilan ma’aikatan gwamnati, kungiyoyin Manoma da Malamai da sauransu.

ADVERTISEMENT

A sakamakon tattaunawar, kwamitocin sun cimma matsaya kan yadda za a kashe kudin, inda suka raba aikin zuwa gida Uku, kamar haka:

Na farko, za a siya buhunan shinkafa guda 40,000 wanda za a tabbatar mutum miliyan 1,050,000 marasa karfi sun amfana da wannan tallafin. Daga cikin biliyan biyun, za a kashe Naira biliyan N1,935,000,000 sannan ragowar Naira Miliyan N65,000,000 za a yi amfani da su wurin tallafawa marasa karfi don zuwa wurin da za a raba abincin.

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Na biyu, za a hada kai da kungiyoyin sufuri kan rage kudin mota don taimakawa mutane wurin zirga-zirgarsu ta yau da kullum. Bayan wannan kuma, gwamnatin za ta siyo motocin sufuri na jihar Kaduna wanda za a rage kudinsu wasu kuma za a barsu shiga kyauta. Bugu da kari, gwamnatin za ta tabbatar ta samar da takin zamani don taimakawa manoma don bunkasa harkar Noma a jihar

Na Karshe, Gwamnan ya bayyana cewa, tuni ya fara tattauna da Sakataren Dindindin na ma’aikatar sufuri kuma zai gana da sabon Ministan sufuri kan yadda za a dawo da layin dogo da ke zirga-zirga acikin jihar wanda ke ta so wa daga Zaria zuwa cikin Kaduna sannan ya nufi Kafanchan.

Gwamnan ya kuma bukaci jama’a da su kara hakuri, ya jaddada aniyar gwamnatin jihar Kaduna wurin nemo mafita don inganta harkoki da rayuwar ‘yan jihar.

Kaduna
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
  • Sulaiman
    Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
  • Sulaiman
    Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
  • Sulaiman
    Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

MASU ALAKA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki
Labarai

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Kaduna
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Kaduna
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Matar Aure Ta Kashe Dan Kishiyarta Mai Kwana 4 A Duniya A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Kaduna

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Kaduna

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.