• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kaduna Za Ta Raba Tallafi Ga Talakawa Sama Da Miliyan Ɗaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Malam Uba Sani, ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta shirya tsaf don fara raba tallafi ga marasa karfi a jihar wadanda cire tallafin fetur ya jefa cikin mawuyacin hali. 

Gwamnatin jihar ta tattauna da shugabannin al’umma game da abun da ya fi cancanta gwamnatin ta yi akan Naira Biliyan biyu da gwamnatin tarayya ta fara bayarwa don tallafawa al’umma.

  • Gwamna Uba Sani Ya Sake Nadin Sabbin Mukamai A Jihar Kaduna 

Kwamitin gwamnatin karkashin jagorancin Mataimakiyar gwamnan, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe ne ya tattauna da shugabannin kungiyoyi masu zaman kansu, wakilan ‘yan kasuwa, wakilan ma’aikatan gwamnati, kungiyoyin Manoma da Malamai da sauransu.

A sakamakon tattaunawar, kwamitocin sun cimma matsaya kan yadda za a kashe kudin, inda suka raba aikin zuwa gida Uku, kamar haka:

Na farko, za a siya buhunan shinkafa guda 40,000 wanda za a tabbatar mutum miliyan 1,050,000 marasa karfi sun amfana da wannan tallafin. Daga cikin biliyan biyun, za a kashe Naira biliyan N1,935,000,000 sannan ragowar Naira Miliyan N65,000,000 za a yi amfani da su wurin tallafawa marasa karfi don zuwa wurin da za a raba abincin.

Labarai Masu Nasaba

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

Na biyu, za a hada kai da kungiyoyin sufuri kan rage kudin mota don taimakawa mutane wurin zirga-zirgarsu ta yau da kullum. Bayan wannan kuma, gwamnatin za ta siyo motocin sufuri na jihar Kaduna wanda za a rage kudinsu wasu kuma za a barsu shiga kyauta. Bugu da kari, gwamnatin za ta tabbatar ta samar da takin zamani don taimakawa manoma don bunkasa harkar Noma a jihar

Na Karshe, Gwamnan ya bayyana cewa, tuni ya fara tattauna da Sakataren Dindindin na ma’aikatar sufuri kuma zai gana da sabon Ministan sufuri kan yadda za a dawo da layin dogo da ke zirga-zirga acikin jihar wanda ke ta so wa daga Zaria zuwa cikin Kaduna sannan ya nufi Kafanchan.

Gwamnan ya kuma bukaci jama’a da su kara hakuri, ya jaddada aniyar gwamnatin jihar Kaduna wurin nemo mafita don inganta harkoki da rayuwar ‘yan jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cire Tallafin feturUba Sani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sassan Kasa Da Kasa Da Za Su Shiga CIFTIS Na Bana Sun Karu Da Kaso Sama Da 20%

Next Post

Matar Aure Ta Kashe Dan Kishiyarta Mai Kwana 4 A Duniya A Bauchi

Related

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

44 minutes ago
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

4 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

4 hours ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

6 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

7 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

10 hours ago
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

Matar Aure Ta Kashe Dan Kishiyarta Mai Kwana 4 A Duniya A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

September 6, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

September 6, 2025
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

September 6, 2025
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

September 6, 2025
‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.