ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Gwamnatin Kano Da NNPP Sun Illata Siyasar Ganduje Duk Da Rashin Nasarar’

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
NNPP

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC na yankin arewa maso yamma, Salihu Lukman ya bayyana cewa ko da ba a samu nasarar cire shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abudullahi Ganduje daga mukaminsa, an yi masa babban illa a siyasar a jiharsa.

Ya kara da cewa dalilin da ya sa gwamnatin Kano da magoya bayan jam’iyyar NNPP suka yi nasarar illata siyasar Ganduje shi ne, lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar ya bar jihar tare da amintattun abokansa.
Lukman ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja mai taken “Hatsarin mummunan shugabancin APC.”

  • Hisbah Ta Ware Wa ‘Yan Jarida Gurbin Mutane 50 A Auren Gata A Kano
  • An Gurfanar Da Mutane 2 A Kotun Sojoji Kan Harin Tudun Biri

An dai kusan shafe wata guda ana yunkurin tsige Ganduje daga mukaminsa. A ranar Alhamis da ta gabata ce, masu zanga-zanga suka mamaye sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, domin neman Ganduje ya sauka daga kan mukaminsa jna shugabancin jam’iyyar, sannan a dawo wa yankin arewa ta tsakiya da mukamin wanda Abudullahi Adamu dan yankin ya rike kafin a bai wa Ganduje.

ADVERTISEMENT

Masu zanga-zanga sun danganta bukatar ne kan dakatarwar da shugabannin mazaba Ganduje suka yi masa kan zargin amsar cin hanci da rashawa da gwamnatin Jihar Kano take yi masa.
Sai dai Lukman ya dage da cewa wannan lamari ba zai faru ba idan da a ce tsohon gwamnan bai dauke amintattun abokansa ba lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar APC suka bar Jihar Kano.

Ya ce, “A lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa, dukkan shugabannin APC na Jihar Kano suka dawo Abuja. Wannan yana daga cikin dalilin da ya sa gwamnatin Jihar Kano ta samu nasarar illata siyasar Ganduje, saboda rashin shuganannin APC a Kano.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

“Gaskiyar magana ita ce, tun lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa tsawon wata tara sau biyu ya je Kano. Jam’iyyar adawa ce ke mulki a jihar kuma yana so APC ta kara kwace Kano.

“Idan har Shugaban kasa, Asiwaju Tinubu wanda yake da ayyuka da yawa zai je Jihar Legas fiye da sau biyar, tabbas abun kunya ne a ce Ganduje ya bayar da uzuri na kasa amfani da mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC na kasa wajen tallata siyasarsa. Raunin siyasa ne ake ya samu nakasu a mahaifarsa,” in ji shi.

Haka kuma dan siyasar na Jihar Kaduna ya zargi Shugaba Tinubu kan ci gaba da mayar da yankin arewa ta tsakiya saniyar ware daga mukamin shugabancinsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025
Tambarin Dimokuradiyya

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Next Post
Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

Bangaren Sauka Na Kumbon Shenzhou-21 Ya Iso Doron Duniya

November 14, 2025
NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.