ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Gwamnatin Kano Da NNPP Sun Illata Siyasar Ganduje Duk Da Rashin Nasarar’

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
NNPP

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC na yankin arewa maso yamma, Salihu Lukman ya bayyana cewa ko da ba a samu nasarar cire shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abudullahi Ganduje daga mukaminsa, an yi masa babban illa a siyasar a jiharsa.

Ya kara da cewa dalilin da ya sa gwamnatin Kano da magoya bayan jam’iyyar NNPP suka yi nasarar illata siyasar Ganduje shi ne, lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar ya bar jihar tare da amintattun abokansa.
Lukman ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja mai taken “Hatsarin mummunan shugabancin APC.”

  • Hisbah Ta Ware Wa ‘Yan Jarida Gurbin Mutane 50 A Auren Gata A Kano
  • An Gurfanar Da Mutane 2 A Kotun Sojoji Kan Harin Tudun Biri

An dai kusan shafe wata guda ana yunkurin tsige Ganduje daga mukaminsa. A ranar Alhamis da ta gabata ce, masu zanga-zanga suka mamaye sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, domin neman Ganduje ya sauka daga kan mukaminsa jna shugabancin jam’iyyar, sannan a dawo wa yankin arewa ta tsakiya da mukamin wanda Abudullahi Adamu dan yankin ya rike kafin a bai wa Ganduje.

ADVERTISEMENT

Masu zanga-zanga sun danganta bukatar ne kan dakatarwar da shugabannin mazaba Ganduje suka yi masa kan zargin amsar cin hanci da rashawa da gwamnatin Jihar Kano take yi masa.
Sai dai Lukman ya dage da cewa wannan lamari ba zai faru ba idan da a ce tsohon gwamnan bai dauke amintattun abokansa ba lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar APC suka bar Jihar Kano.

Ya ce, “A lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa, dukkan shugabannin APC na Jihar Kano suka dawo Abuja. Wannan yana daga cikin dalilin da ya sa gwamnatin Jihar Kano ta samu nasarar illata siyasar Ganduje, saboda rashin shuganannin APC a Kano.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Gaskiyar magana ita ce, tun lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa tsawon wata tara sau biyu ya je Kano. Jam’iyyar adawa ce ke mulki a jihar kuma yana so APC ta kara kwace Kano.

“Idan har Shugaban kasa, Asiwaju Tinubu wanda yake da ayyuka da yawa zai je Jihar Legas fiye da sau biyar, tabbas abun kunya ne a ce Ganduje ya bayar da uzuri na kasa amfani da mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC na kasa wajen tallata siyasarsa. Raunin siyasa ne ake ya samu nakasu a mahaifarsa,” in ji shi.

Haka kuma dan siyasar na Jihar Kaduna ya zargi Shugaba Tinubu kan ci gaba da mayar da yankin arewa ta tsakiya saniyar ware daga mukamin shugabancinsa.

ganduje
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

ganduje
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.