ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Gwamnatin Kano Da NNPP Sun Illata Siyasar Ganduje Duk Da Rashin Nasarar’

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
NNPP

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar APC na yankin arewa maso yamma, Salihu Lukman ya bayyana cewa ko da ba a samu nasarar cire shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abudullahi Ganduje daga mukaminsa, an yi masa babban illa a siyasar a jiharsa.

Ya kara da cewa dalilin da ya sa gwamnatin Kano da magoya bayan jam’iyyar NNPP suka yi nasarar illata siyasar Ganduje shi ne, lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar ya bar jihar tare da amintattun abokansa.
Lukman ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja mai taken “Hatsarin mummunan shugabancin APC.”

  • Hisbah Ta Ware Wa ‘Yan Jarida Gurbin Mutane 50 A Auren Gata A Kano
  • An Gurfanar Da Mutane 2 A Kotun Sojoji Kan Harin Tudun Biri

An dai kusan shafe wata guda ana yunkurin tsige Ganduje daga mukaminsa. A ranar Alhamis da ta gabata ce, masu zanga-zanga suka mamaye sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, domin neman Ganduje ya sauka daga kan mukaminsa jna shugabancin jam’iyyar, sannan a dawo wa yankin arewa ta tsakiya da mukamin wanda Abudullahi Adamu dan yankin ya rike kafin a bai wa Ganduje.

ADVERTISEMENT

Masu zanga-zanga sun danganta bukatar ne kan dakatarwar da shugabannin mazaba Ganduje suka yi masa kan zargin amsar cin hanci da rashawa da gwamnatin Jihar Kano take yi masa.
Sai dai Lukman ya dage da cewa wannan lamari ba zai faru ba idan da a ce tsohon gwamnan bai dauke amintattun abokansa ba lokacin da ya zama shugaban jam’iyyar APC suka bar Jihar Kano.

Ya ce, “A lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa, dukkan shugabannin APC na Jihar Kano suka dawo Abuja. Wannan yana daga cikin dalilin da ya sa gwamnatin Jihar Kano ta samu nasarar illata siyasar Ganduje, saboda rashin shuganannin APC a Kano.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

“Gaskiyar magana ita ce, tun lokacin da Ganduje ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa tsawon wata tara sau biyu ya je Kano. Jam’iyyar adawa ce ke mulki a jihar kuma yana so APC ta kara kwace Kano.

“Idan har Shugaban kasa, Asiwaju Tinubu wanda yake da ayyuka da yawa zai je Jihar Legas fiye da sau biyar, tabbas abun kunya ne a ce Ganduje ya bayar da uzuri na kasa amfani da mukaminsa na shugaban jam’iyyar APC na kasa wajen tallata siyasarsa. Raunin siyasa ne ake ya samu nakasu a mahaifarsa,” in ji shi.

Haka kuma dan siyasar na Jihar Kaduna ya zargi Shugaba Tinubu kan ci gaba da mayar da yankin arewa ta tsakiya saniyar ware daga mukamin shugabancinsa.

ganduje
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Matasa Da Su Dauki Nauyin Zamanantar Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.