Hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano, ta ƙara wa’adin dakatar da nuna wasu fina-finai 22 da aka dakatar da su.
Tun da farko, hukumar ta dakatar da fina-finan ne saboda sun rashin tangance su.
Ta kuma bai wa masu fina-finan mako ɗaya su gyara kurakurensu.
Sai dai yanzu, bayan wani zama da aka yi tsakanin hukumar da wakilan masana’antar Kannywood, an amince a ƙara mako guda domin bai wa masu fina-finan damar gyara fina-finansu, saboda ka da su yi asara.
Shugaban ƙungiyar masu shirya fina-finai ta Nijeriya (MOPPAN) reshen Kano, Ado Ahmad Gidan Dabino, ya ce an samu daidaito bayan ganawa da shugaban hukumar tace fina-finai, Abba Al-Mustapha da wasu jami’ansa.
An shirya sake zama a ranar Alhamis mai zuwa don kammala tattaunawar gaba ɗaya.
Cikin waɗanda suka halarci ganawar har da wakilan MOPPAN kamar su Abdul Amart, Nazifi Asnanic, da Abubakar Bashir Maishadda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp