Gwamnatin Jihar Kano ta buƙaci diyya daga gwamnatin tarayya bisa asarar da ta ce ta fuskanta sakamakon soke bikin Sallah Durbar a jihar na tsawon shekaru biyu a jere.
Kwamishinan harkokin ƙananan hukumomi da Masarautu, Alhaji Tajo Uthman, ne ya bayyana hakan yayin da Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya kai ziyarar Sallah ga Gwamna a gidan gwamnati, a ranar Lahadi.
- Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
- Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Ya ce bikin Durbar ba wai al’ada kaɗai ba ce, illa wani babban ginshiƙi ne na tattalin arziƙin jihar, wanda ke jan hankalin dubban mutane daga cikin gida da wajen ƙasar.
Uthman ya jaddada cewa gwamnati ta riga ta saka kuɗaɗen da ake samu daga bikin Durbar a cikin kasafin kuɗin jihar, kuma soke bikin ya bar giɓin da ya kamata gwamnatin tarayya ta cike.
Tun daga shekarar 2024, rundunar ‘yansandan jihar Kano ta haramta gudanar da bikin Durbar, saboda rikicin masarautar Kano da ke tsakanin Sarki Muhammadu Sanusi II da Sarkin Aminu Ado Bayero, domin hana rikicin rikiɗewa zuwa tashin hankali.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp