ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
12 months ago
Tsadar rayuwa

Al’ummar kasa daga Arewa zuwa Kudu sun gudanar da shagalin bukin muhimmiyar ranar Babbar Sallah a cikin mummunan yanayin tabarbarewar tattalin arziki da ya hanawa bukin sallar armashi.

Bukin sallar layya na zuwa ne kwana daya bayan miliyoyin al’ummar musulmin duniya sun yi hawan Arafat, ranar da ta fi kowace rana daraja a cikin ranakun duniya.

  • Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
  • Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Sallah Babba wadda ake gudanarwa a kowace ranar 10 ga watan Zul -Hijja a fadin duniya bakidaya rana ce ta musamman da al’ummar musulmi ke yanka dabbobi domin koyi da jagoran Annabawa, manzon tsira kuma shugaban talikai, Annabi Muhammad (SAW)

ADVERTISEMENT

Al’umma da dama da suka saba yin layya a baya, a bana suna dauke da tambarin matsaloli a fuskokin su domin kuwa layya ta gagare su a dalilin matsin tattalin arziki wanda ke da alaka da tsauraran manufofin tattalin arziki na gwamnatin Tinubu wadanda al’ummar kasa ke kokawa a kai.

Duk da gwamnatoci a dukkanin matakai sun biya albashin watan Mayu amma ma’aikata da dama ba su samu zarafin gudanar da ibadar layya ba domin albashin ba zai wadace su sayen dabbobi da abinci ba.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

An gudanar da sallah ne bayan da Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III ya bayyana ranar Juma’a 06 ga Yuni a matsayin ranar 10 ga watan Zul-Hijja 1446 a matsayin ranar sallar layya kamar yadda ya bayyana a sanarwar da shugaban kwamitin lamurran addinin musulunci kana Wazirin Sakkwato, Farfesa Sambo Wali Junaid ya sanyawa hannu.

A ra’ayin jama’a da dama ba su da halin sayen dabbobin layya da za su yanka, wasu kuwa sun bayyana cewar ko da suna da halin yin layya to ba ita ce a gaban su ba domin a cewarsu za su shiga cikin gagarumar matsala a gidajen su domin mafi yawa ba su tanadi abincin da iyalansu za su ci ba don haka sayen abinci ne mafi muhimmanci.

Talakawa da daman gaske da kanana da matsakaitan ma’aikata da kananan ‘yan kasuwa sun shaidi sallar layya a wannan shekarar a halin da suke fatar kada Allah ya maimaita domin a ta bakin su ba a taba shaidar sallah a matsin tattalin arziki irin ta wannan shekarar ba.

Tashin gwauron- zabi da dabbobin layya suka yi, hauhawar farashin abinci, tsadar man fetur da halin kuncin da jama’a ke ciki duka abubuwa ne muhimmai da suka taru suka dabaibaye sallar ta hanyar hana mata karsashi.

Gagarumar matsalar tsaro ba dare ba rana daga Borno zuwa Sakkwato, tashin bama- bamai, garkuwa da mutane da kisan gillar da ‘yan ta’adda ke yi wa al’umma ba kakkautawa sun yi matukar tasiri wajen hanawa sallah karsashi.

Rahotanni sun tabbatar da cewar tsananin tsadar da dabbobin layya suka yi ya tilastawa jama’a da dama hakura da yin layya domin abincin da za su ci yana kokarin gagarar su wanda ya zama dalilin da ire-iren wadanda suka samu kudin layya to abinci suke siya wanda shine ya fi muhimmanci.

Auwal Balarabe wani matsakaicin ma’aikaci a Abuja ya bayyana cewar wannan layya ce ta farko a tarihin rayuwarsa da aka yi ba ya da halin yanka dabba wanda a cewarsa ya shiga cikin tarihin da ba zai manta ba a dalilin matsin rayuwa.

Wasu maigidanta a Kano sun bayyana cewar ba za su wahalar da kan su sayen ragon dubu 200 zuwa 250 ba, shanu kuwa sai dubu 500 zuwa miliyan daya don haka suka hakura suka zabi sayen kaji da nama.

Mabambantan al’umma sun bayyana halin rashin da aka fuskanta a wannan shekarar da hauhawar farashin raguna da sauran dabbobin layya ya tilastawa mutane da dama hada kudade domin yin hadakar layya ta hanyar sayen babbarn sa ko saniya wadanda suka kai adadin shekaru biyu na layya.

Wani magudanci Isna’il Abubakar a Sakkwato ya bayyana cewar ragon da ya saya a 2024 a dubu 150 a yanzu sai 260, don haka da shi da makwabta hudu sun hada dubu 800 domin sayen saniya su raba.

Bincike a mabambantan kasuwannin karar dabbobi ya nuna an samu karancin masu sayen raguna, shanu da sauran nau’ukan dabbobi sama da shekarun baya kamar yadda masu sayar da raguna a Abuja, Kano, Bauchi, Kaduna, Neja, Gusau, Sakkwato da Birnin- Kebbi suka bayyanawa manema labarai.

“Ba mu taba ganin sallar da jama’a suka kasa yin tururuwar zuwa sayen dabbobi ba irin wannan shekarar, ko kadan babu ko irin rabin hada-hadar da muka saba samu a shekarun baya.”

A cewar Hassan Mahe ko kadan kasuwar dabbobi a bana ta bambanta da saura domin babu kasuwa, kuma duk da tsadar abincin dabbobi, farashin ya karu ne a dalilin hana shigowa da su daga Nijar da gwamnatin kasar ta yi wanda a kan hakan farashin dabbobin ya ninka.

Baya ga wannan matsalar tsaro wadda ta ki ci ta ki cinyewa gagarumar matsala ce wadda ta hanawa bukin sallah armashi a yankuna da dama da ke fama da matsalar tsaro a kasar nan a dalilin hare- haren ta’addanci.

Haka ma dinbin al’ummar da ke tsugune a sansanin ‘yan gudun hijira ko kadan babu maganar kayatarwar shagalin sallah ko yin layya a wajen su, hasalima ranar sallah kan tuna masu da lokutan baya da suka yi sallah cikin walwala da farin ci a muhallansu kuma a cikin iyalan su.

Kayan abinci kamar shinkafa, masara, gero, dawa, wake, fulawa, man gyada, man-ja da nau’ukan tumatur, albasa, attarugu, tattasai da sauransu sun yi matukar tsada lamarin da tsadar a kullum sai gaba-gaba take yi wanda hakan ya taimaka wajen kara rage armashin sallah domin jama’a da dama ba su da wadatar sayen kayan bukatu.

Maigidanta da dama a tattanawarsu da LEADERSHIP Hausa sun bayyana fatar samun saukin al’amurra ta yadda dabbobi da kayan abinci da na bukatu za su sauko kasa akasin shekaru biyu da suka gabata zuwa yanzu da al’amurra suka tabarbare har jama’a suka shiga cikin kunci maras misaltuwa.

Tsadar rayuwa
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ posts Bio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato
Tsadar rayuwa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Tsadar rayuwa
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Tsadar rayuwa
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.