• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Ta Soke Lasisin Makarantun Masu Zaman Kansu A Jihar Baki Daya

by Sadiq
2 years ago
Kano

Gwamnatin jihar Kano ta soke lasisin duk wasu makarantu masu zaman kansu da ke aiki a jihar.

An yanke hukuncin ne a ranar Asabar yayin wata ganawa da masu makarantu masu zaman kansu.

  • Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba – Jakada
  • Masallacin Zariya: Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kai 12

Mai bai wa gwamna shawara na musamman kan makarantu masu zaman kansu, Alhaji Baba Abubakar Umar ne, ya bayyana cewa ana bukatar dukkan makarantu masu zaman kansu da su yi sabuwar rajista cikin gaggawa.

Umar ya bayyana cewa matakin ya jaddada kudirin gwamnati na ganin cewa makarantu masu zaman kansu sun bi ka’idojin da aka gindaya na gudanar da ayyukansu.

“An tunatar da masu makarantu masu zaman kansu alhakin da ya rataya a wuyansu na biyan harajin kashi 10 ga gwamnati. Wannan kudi ko yaushe yana habaka ci gaba a fannin,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Mashawarcin na musamman ya tabbatar wa duk masu ruwa da tsaki cewa zai tabbatar da adalci wajen kula da ayyukan makarantu masu zaman kansu.

Ya jaddada bukatar aiwatar da ka’idojin aiki ga masu mallakar makarantu masu zaman kansu wadanda suka hada da kayan aiki, yanayin koyo, manhaja da jadawalin koyarwa.

Ya kuma tabbatar wa iyaye fifikon da aka ba su wajen kiyaye muradunsu da na ‘ya’yansu.

Da yake mayar da martani, shugaban kungiyar masu makarantu masu zaman kansu a jihar, Alhaji Muhammad Malam Adamu, ya yaba da matakin da gwamnati ta dauka, yana mai kallon matakin a matsayin abin yabawa a fannin ilimi a jihar.

Adamu ya bayyana muhimmancin yanayin tsarin aiki, yana mai tabbatar da cewa duk wani aiki da ba a bin ka’ida yana samun koma baya.

Ya yi kira ga masu makarantu masu zaman kansu da su hada kai da gwamnati wajen gudanar da sauye-sauyen.

A yayin taron an fitar da wata sabuwar manhaja domin tattara bayanan masu makarantu masu zaman kansu a fadin Kano.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Next Post
Jarin Da Sin Ta Zuba Wa Fannin Layin Dogo Ya Karu Da Kashi 7% A Watanni 7 Na Farkon Bana

Jarin Da Sin Ta Zuba Wa Fannin Layin Dogo Ya Karu Da Kashi 7% A Watanni 7 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.