• Leadership Hausa
Saturday, December 2, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masallacin Zariya: Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kai 12

by Sadiq
4 months ago
in Labarai
0
Masallacin Zariya: Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kai 12
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adadin wadanda suka mutu sakamakon rushewar babban masallacin Zariya, a yammacin ranar Juma’a a garin Zariya na jihar Kaduna, ya kai 12.

Idan za a tuna cewa lamarin ya afku ne a daidai lokacin da masallata suke gudanar da sallar la’asar da misalin karfe 4 na yammacin ranar Juma’a.

  • Tsohon Gwamnan Kwara A Mulkin Soja, Latinwo Ya Kwanta Dama
  • Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

A halin yanzu, gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, da kungiyar Jama’atul Nasir Islam (JNI), sun mika ta’aziyyarsu ga masarautar Zazzau da iyalan wadanda suka rasu.

Gwamna Uba Sani, a cikin ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa, ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka mutu.

Gwamnan ya gode wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, bisa irin rawar da ya taka wajen hada kan al’ummarsa domin gudanar da aikin ceto, da bayar da taimako ga wadanda suka jikkata da kuma jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji

Har Yanzu Ƙanjamau Na Kashe Mutum Guda Duk Bayan Minti Ɗaya – Majalisar Ɗinkin Duniya

Gwamnan ya kuma yaba da kokarin wadanda suka fara yin ceto, da ma’aikatan lafiya, da kuma nagari mutanen Zariya wajen ceto wadanda suka tsira.

Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, ya kuma kara da cewa tuni tawagar manyan jami’an gwamnati karkashin jagorancin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Balarabe Abbas Lawal, ta isa Zariya don tantance halin da ake ciki.

“Gwamnatin jihar za ta kuma bayar da umarnin gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin,” in ji shi.

“Ina matukar bakin ciki da abin da ya faru a babban masallacin Zariya da ke jihar Kaduna, zuciyata na mika sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da wadanda suka jikkata sakamakon rushewar masallacin Zariya.

“Ina kuma mika ta’aziyyata ga Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli, da daukacin al’ummar musulmi bisa wannan rashi. Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa wadanda suka rasu.

“Gwamnatin jihar Kaduna za ta taimaka wa wadanda wannan lamari ya rutsa da su,” in ji shi.

Har ila yau, babban sakataren JNI, Farfesa Khalid Abubakar Aliyu, a wata sanarwa da ya fitar ya yi kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin aukuwar wannan mummunan lamari.

Hakazalika, a sakon ta’aziyyarsa, Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Abbass, ya bayyana wannan mummunan lamari a matsayin abin takaici da ban tausayi.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Musa Abdullahi Krishi ya rabawa manema labarai, shugaban majalisar ya ce “zuciyarsa na alhinin faruwar lamarin, inda ya ce wannan shi ne labari mai ratsa zuciya da ya samu a ‘yan kwanakin nan.

Abbas, wanda ya bayyana alhininsa, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.

Tags: JikkataKadunaRasuwaRushewar MasallaciZariya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Gwamnan Kwara A Mulkin Soja, Latinwo Ya Kwanta Dama

Next Post

Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba – Jakada

Related

Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji
Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji

8 hours ago
Har Yanzu Ƙanjamau Na Kashe Mutum Guda Duk Bayan Minti Ɗaya – Majalisar Ɗinkin Duniya
Manyan Labarai

Har Yanzu Ƙanjamau Na Kashe Mutum Guda Duk Bayan Minti Ɗaya – Majalisar Ɗinkin Duniya

8 hours ago
Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024
Labarai

Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024

9 hours ago
Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2024 Na Biliyan 270
Labarai

Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2024 Na Biliyan 270

10 hours ago
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ke Dauke Da Cutar Kanjamau – Hukumar NACA
Labarai

‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ke Dauke Da Cutar Kanjamau – Hukumar NACA

10 hours ago
CBN Zai Haramta Harkokin Kudi A Asusun Bankin Da Babu BVN Da NIN A 2024
Manyan Labarai

CBN Zai Haramta Harkokin Kudi A Asusun Bankin Da Babu BVN Da NIN A 2024

10 hours ago
Next Post
Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba – Jakada

Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba - Jakada

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Yi Katsalandan A Gwamnatin Ododo Ba – Yahaya Bello

Ba Zan Yi Katsalandan A Gwamnatin Ododo Ba – Yahaya Bello

December 1, 2023
Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji

Gwamna Uba Sani Ya Kafa Kwamitin Binciken Matsalolin Aiki Hajji

December 1, 2023
Har Yanzu Ƙanjamau Na Kashe Mutum Guda Duk Bayan Minti Ɗaya – Majalisar Ɗinkin Duniya

Har Yanzu Ƙanjamau Na Kashe Mutum Guda Duk Bayan Minti Ɗaya – Majalisar Ɗinkin Duniya

December 1, 2023
Sama Da Kamfanoni 5,600 Ne Suka Shiga Baje Kolin Sassan Motoci Na Shanghai

Sama Da Kamfanoni 5,600 Ne Suka Shiga Baje Kolin Sassan Motoci Na Shanghai

December 1, 2023
Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024

Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024

December 1, 2023
Tasirin Cutar HIV A Sin Ya Yi Matukar Raguwa

Tasirin Cutar HIV A Sin Ya Yi Matukar Raguwa

December 1, 2023
Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2024 Na Biliyan 270

Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2024 Na Biliyan 270

December 1, 2023
‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ke Dauke Da Cutar Kanjamau – Hukumar NACA

‘Yan Nijeriya Miliyan 1.8 Ke Dauke Da Cutar Kanjamau – Hukumar NACA

December 1, 2023
CBN Zai Haramta Harkokin Kudi A Asusun Bankin Da Babu BVN Da NIN A 2024

CBN Zai Haramta Harkokin Kudi A Asusun Bankin Da Babu BVN Da NIN A 2024

December 1, 2023
Wakilin Sin Ya Yi Tir Da Matakan Matsin Lamba Da Nufin Dakile Tsarin Jagoranci Da Ci Gaban Duniya

Wakilin Sin Ya Yi Tir Da Matakan Matsin Lamba Da Nufin Dakile Tsarin Jagoranci Da Ci Gaban Duniya

December 1, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.