ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masallacin Zariya: Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kai 12

by Sadiq
3 years ago
Zariya

Adadin wadanda suka mutu sakamakon rushewar babban masallacin Zariya, a yammacin ranar Juma’a a garin Zariya na jihar Kaduna, ya kai 12.

Idan za a tuna cewa lamarin ya afku ne a daidai lokacin da masallata suke gudanar da sallar la’asar da misalin karfe 4 na yammacin ranar Juma’a.

  • Tsohon Gwamnan Kwara A Mulkin Soja, Latinwo Ya Kwanta Dama
  • Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

A halin yanzu, gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, da kungiyar Jama’atul Nasir Islam (JNI), sun mika ta’aziyyarsu ga masarautar Zazzau da iyalan wadanda suka rasu.

ADVERTISEMENT

Gwamna Uba Sani, a cikin ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa, ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka mutu.

Gwamnan ya gode wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, bisa irin rawar da ya taka wajen hada kan al’ummarsa domin gudanar da aikin ceto, da bayar da taimako ga wadanda suka jikkata da kuma jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Gwamnan ya kuma yaba da kokarin wadanda suka fara yin ceto, da ma’aikatan lafiya, da kuma nagari mutanen Zariya wajen ceto wadanda suka tsira.

Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, ya kuma kara da cewa tuni tawagar manyan jami’an gwamnati karkashin jagorancin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Balarabe Abbas Lawal, ta isa Zariya don tantance halin da ake ciki.

“Gwamnatin jihar za ta kuma bayar da umarnin gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin,” in ji shi.

“Ina matukar bakin ciki da abin da ya faru a babban masallacin Zariya da ke jihar Kaduna, zuciyata na mika sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da wadanda suka jikkata sakamakon rushewar masallacin Zariya.

“Ina kuma mika ta’aziyyata ga Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli, da daukacin al’ummar musulmi bisa wannan rashi. Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa wadanda suka rasu.

“Gwamnatin jihar Kaduna za ta taimaka wa wadanda wannan lamari ya rutsa da su,” in ji shi.

Har ila yau, babban sakataren JNI, Farfesa Khalid Abubakar Aliyu, a wata sanarwa da ya fitar ya yi kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin aukuwar wannan mummunan lamari.

Hakazalika, a sakon ta’aziyyarsa, Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Abbass, ya bayyana wannan mummunan lamari a matsayin abin takaici da ban tausayi.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Musa Abdullahi Krishi ya rabawa manema labarai, shugaban majalisar ya ce “zuciyarsa na alhinin faruwar lamarin, inda ya ce wannan shi ne labari mai ratsa zuciya da ya samu a ‘yan kwanakin nan.

Abbas, wanda ya bayyana alhininsa, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba – Jakada

Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba - Jakada

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.