• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Za Ta Ci Gaba Da Sanya Sarakuna Cikin Gudanar Da Shugabanci  – Gwamna Nasir

by Sulaiman and Umar Faruk
11 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kebbi Za Ta Ci Gaba Da Sanya Sarakuna Cikin Gudanar Da Shugabanci  – Gwamna Nasir
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi ya tabbatar wa sarakunan gargajiya cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da sanya su cikin tsare-tsaren gudanar da mulki da kuma shirye -shiryen ci gaba don inganta rayuwar al’umma.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da tawagar al’ummar garin Besse ta kai masa ziyarar godiya a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi, domin nuna jin dadin nadin Farfesa Tijjani Muhammad Bande a matsayin sabon Uban kasar Besse (Barade na biyu) da ke karamar hukumar Koko-Besse.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Kasuwar Dodoru A Jihar Kebbi, Rumfuna Da Yawa Sun Lalace
  • Zanga-zanga: Daga Tutar Rasha Cin Amanar Kasa Ne – Janar Musa

Gwamna Nasir ya jaddada kudirin gwamnatinsa na shigar da Sarakunan cikin shirye-shiryen raya jihar da kasa baki daya, inda ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta amince da aikin gyaran hanyar Koko-Besse zuwa Zariya-Kalakala zuwa Bagudo, kuma nan ba da jimawa ba, za a fara aikin hanyar.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Ya kuma bayyana shirin bunkasa garuruwan yankin da sauran sassan jihar bayan kammala aikin gyaran fuska na babban birnin jihar. Ya kara da cewa, gwamnati za ta gyara makarantu 30 zuwa 50 a Koko-Besse domin inganta ilimi a yankin.

 

Har ilayau, Gwamnan ya taya Farfesa Bande murnar nadin da aka yi masa, inda ya bayyana shi a matsayin fitaccen malami kuma jami’in diflomasiyya wanda ya yi hasashe tare da daukaka martabar jihar Kebbi da Nijeriya a fagen kasa da kasa. Ya kuma bai wa Farfesa Bande tabbacin goyon bayansa wajen tafiyar da mulkin al’ummarsa cikin nasara.

 

Tun da farko, a jawabinsu, Uban kasa, kuma Dutsinmari, Alhaji Muhammadu Mu’allah’yidi Usman da Farfesa Abubakar Abdullahi Bagudo a madadin al’ummar Besse sun gode wa Gwamna Nasir Idris bisa amincewa da nadin Farfesa Bande. Sun bayyana gamsuwarsu kan yadda Farfesa Bande zai iya yin amfani da kwarewarsa da iliminsa wajen bunkasa gundumar tare da yin kira ga gwamnan da ya ba sabon Uban kasar goyon baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CHINADA Ta Nuna Shakku Ga Hukuncin Da Aka Yanke Kan Dan Wasan Tsalle-tsalle Da Guje-guje Na Amurka Game Da Shan Maganin Kara Kuzari

Next Post

Duk Wanda Ya Bar Gida, Gida Ya Bar Shi

Related

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

8 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

10 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

14 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

16 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

16 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

17 hours ago
Next Post
Duk Wanda Ya Bar Gida, Gida Ya Bar Shi

Duk Wanda Ya Bar Gida, Gida Ya Bar Shi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.