• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kebbi Za Ta Ci Gaba Da Sanya Sarakuna Cikin Gudanar Da Shugabanci  – Gwamna Nasir

by Sulaiman and Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Kebbi Za Ta Ci Gaba Da Sanya Sarakuna Cikin Gudanar Da Shugabanci  – Gwamna Nasir
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Nasir Idris na jihar Kebbi ya tabbatar wa sarakunan gargajiya cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da sanya su cikin tsare-tsaren gudanar da mulki da kuma shirye -shiryen ci gaba don inganta rayuwar al’umma.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da tawagar al’ummar garin Besse ta kai masa ziyarar godiya a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi, domin nuna jin dadin nadin Farfesa Tijjani Muhammad Bande a matsayin sabon Uban kasar Besse (Barade na biyu) da ke karamar hukumar Koko-Besse.

  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Kasuwar Dodoru A Jihar Kebbi, Rumfuna Da Yawa Sun Lalace
  • Zanga-zanga: Daga Tutar Rasha Cin Amanar Kasa Ne – Janar Musa

Gwamna Nasir ya jaddada kudirin gwamnatinsa na shigar da Sarakunan cikin shirye-shiryen raya jihar da kasa baki daya, inda ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta amince da aikin gyaran hanyar Koko-Besse zuwa Zariya-Kalakala zuwa Bagudo, kuma nan ba da jimawa ba, za a fara aikin hanyar.

 

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Ya kuma bayyana shirin bunkasa garuruwan yankin da sauran sassan jihar bayan kammala aikin gyaran fuska na babban birnin jihar. Ya kara da cewa, gwamnati za ta gyara makarantu 30 zuwa 50 a Koko-Besse domin inganta ilimi a yankin.

 

Har ilayau, Gwamnan ya taya Farfesa Bande murnar nadin da aka yi masa, inda ya bayyana shi a matsayin fitaccen malami kuma jami’in diflomasiyya wanda ya yi hasashe tare da daukaka martabar jihar Kebbi da Nijeriya a fagen kasa da kasa. Ya kuma bai wa Farfesa Bande tabbacin goyon bayansa wajen tafiyar da mulkin al’ummarsa cikin nasara.

 

Tun da farko, a jawabinsu, Uban kasa, kuma Dutsinmari, Alhaji Muhammadu Mu’allah’yidi Usman da Farfesa Abubakar Abdullahi Bagudo a madadin al’ummar Besse sun gode wa Gwamna Nasir Idris bisa amincewa da nadin Farfesa Bande. Sun bayyana gamsuwarsu kan yadda Farfesa Bande zai iya yin amfani da kwarewarsa da iliminsa wajen bunkasa gundumar tare da yin kira ga gwamnan da ya ba sabon Uban kasar goyon baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CHINADA Ta Nuna Shakku Ga Hukuncin Da Aka Yanke Kan Dan Wasan Tsalle-tsalle Da Guje-guje Na Amurka Game Da Shan Maganin Kara Kuzari

Next Post

Duk Wanda Ya Bar Gida, Gida Ya Bar Shi

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

5 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

8 hours ago
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo
Labarai

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

11 hours ago
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet
Labarai

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

13 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

15 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

19 hours ago
Next Post
Duk Wanda Ya Bar Gida, Gida Ya Bar Shi

Duk Wanda Ya Bar Gida, Gida Ya Bar Shi

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.