• English
  • Business News
Friday, June 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Legas Ta Bayar Da Karin Jiragen Ruwa Yayin Da Dokar Hana Okada Ta Fara Aiki

by Muhammad
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Legas Ta Bayar Da Karin Jiragen Ruwa Yayin Da Dokar Hana Okada Ta Fara Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da gwamnatin jihar Legas ta fara aiwatar da dokar hana zirga-zirgar baburan kasuwanci da aka fi sani da Okada a ranar Laraba, hukumar kula da jiragen ruwa ta Legas (LAGFERRY) ta ce ta tura karin jiragen ruwa don kara tafiye-tafiyen aiki na yau da kullun a tashoshi da jiragen ruwa da ke yankunan da abin ya shafa.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa dokar hana gudanar da ayyukan Okada ta shafi kananan hukumomi shida da kuma kananan hukumomi tara kebantattu (LCDAs) na jihar.

  • Tashar Samar Da Lantarki Daga Hasken Rana Da Igiyar Ruwa Ta Farko a Kasar Sin Ta Fara Aiki

A halin da ake ciki, gwamnatin jihar Legas ta ce babu bukatar damuwa kan shirin aiwatar da dokar hana Okada.

Kwamishinan yada labarai da dabaru, Gbenga Omotosho, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce an samar da matakan dakile duk wani hargitsi, inda ya ce za a aiwatar da dokar ba tare da wata tangarda ba.

“Babu bukatar damuwa game da aiwatar da dokar, wanda akasarin mutanen Legas ke yabawa a matsayin karfafa dokar zirga-zirgar Legas 2012 (wanda aka gyara a 2018),” in ji Kwamishinan.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

Idan za a iya tunawa, a ranar 18 ga watan Mayun 2022, Gwamna Babajide Sanwo-Olu, ya sanar da dakatarwar a wani taro da kwamishinan ‘yan sandan jihar, da kwamandojin yankin da kuma jami’an ‘yan sanda na shiyyar a fadar gwamnati dake Alausa.

Daga ranar Laraba 1 ga watan Yuni 2022, gwamnan ya umurci jami’an tsaro da su aiwatar da dokar hana fita a fadin yankunan da abin ya shafa: Eti-Osa, Ikeja, Surulere, Lagos Island, Lagos Mainland, da Apapa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin LegasJiragen RuwaLegasOkada
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Real Madrid 4 Na Cikin ‘Yan Wasan Champions Legue 11 A Wannan Shekarar

Next Post

Sojoji Sun Ragargaji ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno

Related

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 
Manyan Labarai

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

18 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

1 hour ago
Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo

2 hours ago
Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma
Manyan Labarai

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

3 hours ago
An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya
Manyan Labarai

An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

4 hours ago
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba
Manyan Labarai

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

19 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Ragargaji ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno

Sojoji Sun Ragargaji 'Yan Ta'adda A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

June 20, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Filato, Mutane 15 Sun Mutu A Bokkos Da Mangu

June 20, 2025
Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo

Ƴansanda Sun Bankaɗo Maɓoyar Masu Garkuwa Da Mutane A Ondo

June 20, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

June 20, 2025
Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6

Nico Williams Ya Amince Da Komawa Barcelona Akan Kwantiragin Shekaru 6

June 20, 2025
Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

Majalisa Na Binciken Yadda Aka Kashe Naira Tiriliyan 1.12 Na Tallafin Manoma

June 20, 2025
An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

An Nemi A Kafa Dokar Ta-ɓaci Kan Masu Ƙwacen Waya

June 20, 2025
Sojoji Sun DaÆ™ile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

Sojoji Sun DaÆ™ile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe 8 A Katsina

June 20, 2025
Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya: Akwai Babban Aiki A Gaban Nijeriya

June 20, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Asibiti, Motocin Bas Na CNG A Kaduna

June 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.