• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ba Ta Runtsawa Saboda Matsalar Tsaro – Minista

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Nijeriya Ba Ta Runtsawa Saboda Matsalar Tsaro – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya ce gwamnatin tarayya na yin namijin kokari wajen yaki da kalubalen tsaro da ke addabar Nijeriya.

 

Tunji-Ojo ya bayyana hakan ne a ranar Talata a gidan talabijin na Channels, inda ya ce mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, da ministan tsaro, Mohammed Badaru da babban hafsan tsaro, Janar Christopher Musa, ba sa runtsawa saboda matsalar tsaron kasar nan.

  • Sin Ta Kafa Tsarin Ilimin Koyar Da Sana’o’i Mafi Girma A Duniya
  • Mutfwang Ya Amince Da Mafi Karancin Albashi Na N70,000 Ga Ma’aikatan Filato

“Ba wanda yake hutawa a tsakanin, Malam Nuhu Ribadu da ministan tsaro da shugaban hafsan tsaro da kuma shugaban hukumar farin kaya (DSS).

 

Labarai Masu Nasaba

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

“Ba wanda yake barci, muna aiki tukuru. Wannan batu na tsaro babban al’amari ne da ya shafi kasa baki daya, kuma ba zan zauna a nan na ki sauke nauyin tsaron ‘yan Nijeriya a madadin shugaban kasa ba,” in ji Ministan.

 

A cewarsa, an samu ingantuwar tsaro a kasar nan tun bayan hawan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, inda ya kara da cewa sojoji sun durkusar da ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP a yankin arewa maso gabas.

 

Ya kuma yi nuni da cewa gwamnati mai ci ta kasance abun misali wajen tabbatar da tsaro da rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya.

 

Ministan wanda ya yi la’akari da harin da wata sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda ta kai a jihohin Sakkwato da Kebbi, ya bukaci ‘yan Nijeriya da ka da su yi wa Tinubu hukunci kan lamarin, yana mai cewa shugaban kasar na sane da kalubalen tsaro.

 

“Shugaban kasa yana kula da wadannan batutuwa. Ka da ku yi wa shugaban kasa hukunci, ko wannan gwamnati da wadannan mataki. Yin magana na da sauki, amma daukan mataki shi ne ke da sauri.

 

“Mun zo ranar 29 ga Mayu a shekarar da ta gabata, ba na son mu kawo siyasa cikin wannan. Dukanmu mun san halin da ake ciki a fadin kasar nan, shin mun isa inda muke son isa? Amsar ita ce a’a. Muna inda muka kasance? Amsar ita ce a’a. Mun samu ci gaba,” in ji Tunji-Ojo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Su Wane Ne Lakurawa? Daga Ina Suke? Me Cece Akidarsu?

Next Post

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (1)

Related

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
Labarai

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

1 hour ago
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

3 hours ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

5 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

7 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

9 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

9 hours ago
Next Post
SAW

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (1)

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.