• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ba Ta Runtsawa Saboda Matsalar Tsaro – Minista

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Nijeriya Ba Ta Runtsawa Saboda Matsalar Tsaro – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya ce gwamnatin tarayya na yin namijin kokari wajen yaki da kalubalen tsaro da ke addabar Nijeriya.

 

Tunji-Ojo ya bayyana hakan ne a ranar Talata a gidan talabijin na Channels, inda ya ce mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, da ministan tsaro, Mohammed Badaru da babban hafsan tsaro, Janar Christopher Musa, ba sa runtsawa saboda matsalar tsaron kasar nan.

  • Sin Ta Kafa Tsarin Ilimin Koyar Da Sana’o’i Mafi Girma A Duniya
  • Mutfwang Ya Amince Da Mafi Karancin Albashi Na N70,000 Ga Ma’aikatan Filato

“Ba wanda yake hutawa a tsakanin, Malam Nuhu Ribadu da ministan tsaro da shugaban hafsan tsaro da kuma shugaban hukumar farin kaya (DSS).

 

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

“Ba wanda yake barci, muna aiki tukuru. Wannan batu na tsaro babban al’amari ne da ya shafi kasa baki daya, kuma ba zan zauna a nan na ki sauke nauyin tsaron ‘yan Nijeriya a madadin shugaban kasa ba,” in ji Ministan.

 

A cewarsa, an samu ingantuwar tsaro a kasar nan tun bayan hawan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, inda ya kara da cewa sojoji sun durkusar da ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP a yankin arewa maso gabas.

 

Ya kuma yi nuni da cewa gwamnati mai ci ta kasance abun misali wajen tabbatar da tsaro da rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya.

 

Ministan wanda ya yi la’akari da harin da wata sabuwar kungiyar ‘yan ta’adda ta kai a jihohin Sakkwato da Kebbi, ya bukaci ‘yan Nijeriya da ka da su yi wa Tinubu hukunci kan lamarin, yana mai cewa shugaban kasar na sane da kalubalen tsaro.

 

“Shugaban kasa yana kula da wadannan batutuwa. Ka da ku yi wa shugaban kasa hukunci, ko wannan gwamnati da wadannan mataki. Yin magana na da sauki, amma daukan mataki shi ne ke da sauri.

 

“Mun zo ranar 29 ga Mayu a shekarar da ta gabata, ba na son mu kawo siyasa cikin wannan. Dukanmu mun san halin da ake ciki a fadin kasar nan, shin mun isa inda muke son isa? Amsar ita ce a’a. Muna inda muka kasance? Amsar ita ce a’a. Mun samu ci gaba,” in ji Tunji-Ojo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Su Wane Ne Lakurawa? Daga Ina Suke? Me Cece Akidarsu?

Next Post

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (1)

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

17 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

24 hours ago
Next Post
SAW

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (1)

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.