ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ta Bayar Da Tirela 100 Na Shinkafa, Dawa Da Masara A Raba A Kano

by Muhammad
2 years ago
Kano

Gwamnatin tarayya ta bai wa gwamnatin jihar Kano tallafin tirela 100 na shinkafa da tirela 44 na dawa da kuma tirelar masara hudu don rabawa mabukata a jihar.

Daraktan yada labaran gwamnatin Kano, Sanusi Dawakin Tofa, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai ranar Lahadi a Kano.

  • Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba
  • Ramadan: ‘Yan Kasuwa Sun Koka Kan Samun Ƙarancin Ciniki A Kano

Ya ce gidauniyar Dangote ta kuma tallafa wa jihar da buhunan shinkafa 10,000 120,000.

ADVERTISEMENT

“Baya ga wannan tallafin, gwamnatin jihar ta bayar da tirela 145 na hatsi iri-iri domin rabawa ga kananan hukumomi 44 da mazabu 484,” inji shi.

Tofa ya ce sun yi hakan ne tare da hadin guiwar kananan hukumomin jihar.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Ya ce gwamnatin jihar ta kuma fara gudanar da bincike kan shirin ciyarwa na watan Ramadan da ake yi a jihar.

Tofa ya ce Gwamna Abba Yusuf ya nuna rashin jin dadinsa kan yadda shirin ke gudana a lokacin da ya kai ziyarar ba-zata zuwa wasu zababbun cibiyoyin ciyarwar azumin da ke cikin birnin Kano.

” Yusuf ya nuna rashin jin dadinsa da abin da ya gani a cibiyoyin, inda ya yi tambayoyi da dama wadanda ba su da amsoshi daga masu gudanar da aikin abincin.

“Gwamnan ya ce nan da sa’o’i 24 masu zuwa, gwamnati za ta sake tsara kwamitin ciyar da abinci don gudanar da aikin,” in ji shi.

Tofa ya ce gwamnatin jihar ta kebe cibiyoyi 80 na ciyar da abinci a kananan hukumomi takwas, kuma manufar ita ce ciyar da mutane 1,000 a kowace cibiya.

“Yusuf ya ziyarci wasu cibiyoyin da ke aikin ciyar da abincin, ya ga abin da ke faruwa, inda ya tarar da sabanin abunda suka tsara na ciyar da mutane 1,000 da aka yi niyya a kullum, sai suka samu mutane 450 ne kadai ke cin gajiyar ciyarwar a cibiyoyin da ya ziyarta,” inji shi.

Tofa ya ce saboda halin da ake ciki a cibiyoyin, gwamnan ya ba da umarnin sake tsara kwamitin da zai tafiyar da aikin.

Ya kuma bayar da umarnin gudanar da bincike kan dukkan masu hannu a ciki don hukunta wadanda aka kama da aikata laifi a aikin ciyarwar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, Ɗalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Karɓi ‘Yansanda Masu Horo Na Musamman 200 Da Motocin Yaƙi 2

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.