ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Dangote Ke Ciyar Da Mutum 10,000 Kullum A Kano Baya Ga Buhun Shinkafa Miliyan 1 Da Ya Raba

by yahuzajere
2 years ago
dangote

Attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya kaddamar da rabon abinci kyauta ga al’ummar Musulmi akalla 10,000 a Jihar Kano, jiharsa ta asali, ta hannun Gidauniyar Aliko Dangote.

Har ila yau, gidauniyar ta fadada karamcin ta hanyar raba buhunan shinkafa miliyan daya da kudinsu ya haura Naira biliyan 13 a fadin jihohi 36 na tarayya da Babban Birnin Tarayya Abuja domin rage yunwa a kasar nan.

Manufar wannan tallafi ita ce a sassauta wa miliyoyin ‘yan Nijeriya matsin da suke sha sakamakon kalubalen tattalin arziki da kasar ke fama da shi.

ADVERTISEMENT

Wannan duka kari ne a kan rabon burodi 20,000 a kullum ga mazauna Kano da kuma wasu 15,000 ga mazauna Legas, inda tsarin ciyarwar da aka fara kuma ya dore tun daga 2020 a lokacin annobar COVID-19.

Abincin da ake dafawa na buda-bakin Ramadan kyauta ya hada da shinkafa dafa-duka, farar shinkafa da miya, taliya dafa-duka, doya, wake da naman kaza da na saniya, kana da ruwan sha na gora ga kowane mutum.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

  • ‘Yan Ta’adda Sun Sake Sace Mutane 87 A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Kaduna

Ana raba kunshin abincin ne a masallatan Juma’a da tituna da gidajen yari da gidajen marayu da gidajen riman (na tsare mutane) da sauran wurare a cikin birnin Kano da kewaye.

Wani da ya ci gajiyar abincin mai suna Musa Maikatako, mazaunin Tarauni ya nuna jin dadinsa da wannan karimcin wanda ya ce ya taimaka masa wajen yin buda baki cikin sauki.

Maikatako, wanda a bayyane fuskarsa na cike da farin ciki, ya ce abinci na kyauta ya kawar da wahalhalun da jama’a da dama za su iya fusktan wajen yin buda baki da ruwa kawai, ba tare da abinci ba, bisa la’akari da halin kuncin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

“Ba zan iya bayyana irin farin cikin da nake ciki ba, wannan abincin zai taimaka matuka wajen taimaka wa talakawa kamar ni mu samu abin da za mu yi buda baki da abinci mai nauyi.

“Na san mutane da yawa a jihar nan wadanda za su iya yin buda baki da ruwa kawai. Don haka wannan abincin ya kawo sauki kwarai da gaske,” in ji shi.

Da yake nuna farin cikinsa, Maikatako ya nuna godiya ga Gidauniyar Dangote bisa wannan karamcin, inda ya yi addu’ar Allah ya kara masa arziki, ya kuma ci gaba da sanya albarka a kasuwancinsa.

Har ila yau, wata da ta ci gajiyar tallafin, Hajiya Inna Tukur, ta bayyana jin dadin ta da rabon abincin, wanda a cewarta Gidauniyar Aliko Dangote ta kawo mata dauki.

A cewar Inna, ta yi farin ciki da irin wannan abinci mai dadi da ake ba ta kyauta a halin matsin da ake ciki.

“A cikin wahalhalun da ake fama wanda yana da kamar wuya mu iya cin abinci ko da sau biyu a rana, amma sai ga shi cikin ludufi, an samu wani yana taimaka mana da abinci mai lagwada, gaskiya wannan ba karamin abu ba ne.

“Ba abin da zan ce sai dai in yi godiya ga ku da Aliko Dangote, ina rokon Allah ya kara muku albarka.”

Baya ga rabon burodi da aka kwashi tsawon shekara 4 ana yi kyauta, Gidauniyar Dangote ta shafe sama da shekaru 30 tana ciyar da mabukata a Kano. Ana yin hakan ne daga gidan mahaifiyarsa da ke Koki da kuma wasu wuraren dafa abinci daban-daban. Wannan shiri na ciyarwa yana ciyar da mazauna Kano 10,000 a kullum tun daga karin kumallo, abincin rana, da kuma abincin dare tsawon shekara 30 ba fashi.

 

 

dangote
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

dangote
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
dangote
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Bayan Kwance Alakar Soji Da Faransa, Nijar Ta Sake Raba Gari Da Sojin Amurka 

Bayan Kwance Alakar Soji Da Faransa, Nijar Ta Sake Raba Gari Da Sojin Amurka 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.