• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Nijeriya Ta Nuna Halin Ko-in-kula A Lokacin Da Nake Tsare A Kurkukun Kasar Nijar -442

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
Gwamnatin Nijeriya Ta Nuna Halin Ko-in-kula A Lokacin Da Nake Tsare A Kurkukun Kasar Nijar -442
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matashin mawakin gambara dan asalin Zaria da ke Jihar Kaduna, Mubarak Abdulkarim wanda aka fi sani da 442 a wata hira da yayi da jarumar Kannywood Hadiza Gabon a cikin shirinta na Gabon’s Room Talk Show ya bayyana yadda gwamnatin Nijeriya ta nuna halin ko in kula a kan tsare shi da aka yi a kasar Nijar bayan samunsa da laifin yin biza ba bisa ka’ida ba.

442 ya tabbatar da cewar duk da cewar wasu ‘yan kasar Nijar ne suka damfareshi wajen nema masa bizar zama a kasar da ke yammacin Afirika, inda daga baya suka gudu bayan sun gano cewar hukuma tana bincike a kan lamarin, hakan bai sa gwamnatin Nijeriya ta hannun ofishin jakadancin kasar da ke kasar Nijar su saka baki wajen nema masu ‘yanci ba.

  • ‘Yan Boko Haram Sun Sake Lalata Layukan Wutar Lantarki Mai Karfin 330KVA A Yobe
  • Kwalliya A Cikin Gida

‘’Haka nan dai muka ci gaba da gwagwarmaya da sauran yan uwa da masoya wajen ganin mun shaki iskar ‘yanci bayan shafe watanni a tsare a gidan gyaran hali a kasar Nijar’’ inji 442.

Da yake amsa tambaya a kan ko ya rabu da abokiyar aikinsa Safara’u wadda aka sansu tare kafin ya hadu da wannan iftila’i a kasar Nijar, Mubarak ya tabbatar da cewa ko kusa ba shida wata matsala da Safara’u illa dai yanzu kowa a cikinsu ya kama wata sabgar wadda yake ganin ta fiye masa.

Amma a kowane lokaci na bukaci in yi aiki da ita kokuma ita da kanta ta bukaci ta dawo wajena kofa a bude take domin in amshe ta mu ci gaba daga inda muka tsaya, saboda naga cewar  tanada fasahar waka kuma tana da sha’awar yin aiki tare dani inda take samun goyon bayan iyayenta.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

442 ya kara da cewar har yanzu da yake wannan maganar bai yi danasanin aikata abinda ya janyo aka daureshi a gidan gyaran hali na kasar Nijar ba, domin kuwa aiki ne ya kai shi kuma wannan ce hanyar neman abincinsa kuma kowa zai iya fuskantar kalubale a kan hanyarsa ta neman abinci.

Daga karshe Mubarak ya bukaci mutane masu yi masa kallon wani wanda yake bata tarbiyar matasa ta hanyar wakokinsa da su daina aibata abinda yake yi illa dai su dinga yi masa addu’a su kuma bashi shawara idan sunga wani kuskure domin ko kadan bashida wata manufa ta bata tarbiyar matasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matsalolin Da Ke Faruwa Tsakanin Mata Masu Aiki Da Mazajensu

Next Post

‘Yan Boko Haram Sun Sake Lalata Layukan Wutar Lantarki Mai Karfin 330KVA A Yobe

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

6 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

3 weeks ago
Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban ÆŠauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

3 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

4 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

4 weeks ago
Next Post
‘Yan Boko Haram Sun Sake Lalata Layukan Wutar Lantarki Mai Karfin 330KVA A Yobe

‘Yan Boko Haram Sun Sake Lalata Layukan Wutar Lantarki Mai Karfin 330KVA A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
442

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.