• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

by Abubakar Abba
1 year ago
Google

Gwamnatin Tarayya ta yi hadaka da kamfanin Google, domin kaddamar da shirin bayar da horo, bisa nufin tallafawa matasan kasar, masu yin sana’ar kirkira, guda 2,500.

Ta yi wannan hadakar ce, ta hanyar ma’aikatar kula da Al’adu da fannin kirkirar tattalin arziki.

  • Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano
  • Super Eagles Ta Hauro Matsayi Na 36 A Jadawalin Duniya Na FIFA

Ana kuma sa ran a nan gaba, akalla wadanda za su amfana da shirin, za su kai yawan biliyan 10,000.

Cibiyar baya da horon kirkira ta Del York ce, za ta wanzar da shirin.

Hakazalika, shirin zai mayar da hankali ne, wajen bunkasa fasahar kirkira da kuma kara karfafa guiwar yin kirkira da kuma habaka yin da kamfanoni masu zaman kansu, da ke a fannin masana’antar kikira a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

Shirin wanda ma’aiktar kula da al’adu tare cibiyar ma’aikatar al’adu ta kasa NCAC da kuma CLAP da za su wanzar da shi.

Babbar manufar shirin shi ne, don a karfafa guiwar matasa masu sha’awar fannin kirkira a kasar nan.

Ta hanyar yin hadaka da kamfanin na Google da Del York, wadanda za su amfana da horon, za a horas da su a bangarori kamar na wajen yin finafinai da sauransu.

Da take yin jawabi a kan mahiimancin hadakar ministan ma’aikatar kula da al’adu Hannatu Musa-Musawa, ta bayyana jin dadinta a kan wannan hadakar.

A cewarta, wannan hadakar, ta nuna yunkurin da ake da shi a kasar nan, na kara habaka zakakuran matasan da ke a fannin kir-kira a kasar.

Ta ce, samar da kayan aikin ga matasan da ke a fanin na kir-kira, ba wai kawai don a samar da ayyukan yi bane, har da ma kara daga darajar Nijeriya don ta zamo a kan gaba a duniya, a fannin wajen daga darajar al’adu.

Hannutu ta sanar da cewa, shirin na daya daga cikin kudurorin gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu da a turance, ake kira da Renewed Hope agenda, ta yadda za a tallafawa matasan da ke a fannin kir-kira, domin suma su bayar da ta su gudanmawar, wajen kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Haron na mako shida, zai samarwa wadanda za su amfana wani ginshiki kwarewa na yin kir-kira na sarrafa fina-finan bidiyo da sarrafa hotuna da sauransu.

Bugu da kari, daga cikn wadanda aka zabo, za a kuma bayar da wani horon na mako uku.

Olumide Falegan, manaja a sashen al’adu a kamfanin Google, ya jaddada mahimmanci da shirin yake da shi.

Ya ce, shirin zai taimaka wajen gano matasa da ke da kwarewa a masana’antar kirkira.

A cewarsa, baya ga tallafa kwarrun matasan su 2,500, ana kuma sa ran za’a kara fadada shirin zuwa ga matasa 10,000 da suma za su amfana a daukacin fadin kasar.

Shi kuwa babban shugaban rukunonin Del York Linus Idahosa, ya bayyana cewa, hadakar za ta ci ke gibin da ak da shin a samar da kwararu da masu ruwa da tsaki a fannin kir-kira.

An dai fara karbar takardun shiga shirin wadda aka bude a ranar 8 na watan Okutobar 2024, za kuma rufe karbar, a ranar 30n ga watan na Okutobar 2024.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025
Tattalin Arziki

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Next Post
Kashi 4.1 Na ‘Yan Nijeriya Ne Kawai Za Su Amfana Da Tsarin Mafi Karancin Albashi —Bankin Duniya

Kashi 4.1 Na ‘Yan Nijeriya Ne Kawai Za Su Amfana Da Tsarin Mafi Karancin Albashi —Bankin Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.