ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

by Abubakar Abba
2 years ago
Google

Gwamnatin Tarayya ta yi hadaka da kamfanin Google, domin kaddamar da shirin bayar da horo, bisa nufin tallafawa matasan kasar, masu yin sana’ar kirkira, guda 2,500.

Ta yi wannan hadakar ce, ta hanyar ma’aikatar kula da Al’adu da fannin kirkirar tattalin arziki.

  • Sarki Sanusi II Zai Naɗa Babban Ɗansa A Matsayin Ciroman Kano
  • Super Eagles Ta Hauro Matsayi Na 36 A Jadawalin Duniya Na FIFA

Ana kuma sa ran a nan gaba, akalla wadanda za su amfana da shirin, za su kai yawan biliyan 10,000.

ADVERTISEMENT

Cibiyar baya da horon kirkira ta Del York ce, za ta wanzar da shirin.

Hakazalika, shirin zai mayar da hankali ne, wajen bunkasa fasahar kirkira da kuma kara karfafa guiwar yin kirkira da kuma habaka yin da kamfanoni masu zaman kansu, da ke a fannin masana’antar kikira a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Shirin wanda ma’aiktar kula da al’adu tare cibiyar ma’aikatar al’adu ta kasa NCAC da kuma CLAP da za su wanzar da shi.

Babbar manufar shirin shi ne, don a karfafa guiwar matasa masu sha’awar fannin kirkira a kasar nan.

Ta hanyar yin hadaka da kamfanin na Google da Del York, wadanda za su amfana da horon, za a horas da su a bangarori kamar na wajen yin finafinai da sauransu.

Da take yin jawabi a kan mahiimancin hadakar ministan ma’aikatar kula da al’adu Hannatu Musa-Musawa, ta bayyana jin dadinta a kan wannan hadakar.

A cewarta, wannan hadakar, ta nuna yunkurin da ake da shi a kasar nan, na kara habaka zakakuran matasan da ke a fannin kir-kira a kasar.

Ta ce, samar da kayan aikin ga matasan da ke a fanin na kir-kira, ba wai kawai don a samar da ayyukan yi bane, har da ma kara daga darajar Nijeriya don ta zamo a kan gaba a duniya, a fannin wajen daga darajar al’adu.

Hannutu ta sanar da cewa, shirin na daya daga cikin kudurorin gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu da a turance, ake kira da Renewed Hope agenda, ta yadda za a tallafawa matasan da ke a fannin kir-kira, domin suma su bayar da ta su gudanmawar, wajen kara bunkasa tattalin arzikin Nijeriya.

Haron na mako shida, zai samarwa wadanda za su amfana wani ginshiki kwarewa na yin kir-kira na sarrafa fina-finan bidiyo da sarrafa hotuna da sauransu.

Bugu da kari, daga cikn wadanda aka zabo, za a kuma bayar da wani horon na mako uku.

Olumide Falegan, manaja a sashen al’adu a kamfanin Google, ya jaddada mahimmanci da shirin yake da shi.

Ya ce, shirin zai taimaka wajen gano matasa da ke da kwarewa a masana’antar kirkira.

A cewarsa, baya ga tallafa kwarrun matasan su 2,500, ana kuma sa ran za’a kara fadada shirin zuwa ga matasa 10,000 da suma za su amfana a daukacin fadin kasar.

Shi kuwa babban shugaban rukunonin Del York Linus Idahosa, ya bayyana cewa, hadakar za ta ci ke gibin da ak da shin a samar da kwararu da masu ruwa da tsaki a fannin kir-kira.

An dai fara karbar takardun shiga shirin wadda aka bude a ranar 8 na watan Okutobar 2024, za kuma rufe karbar, a ranar 30n ga watan na Okutobar 2024.

Google
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Next Post
Kashi 4.1 Na ‘Yan Nijeriya Ne Kawai Za Su Amfana Da Tsarin Mafi Karancin Albashi —Bankin Duniya

Kashi 4.1 Na ‘Yan Nijeriya Ne Kawai Za Su Amfana Da Tsarin Mafi Karancin Albashi —Bankin Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.